Rundunar Tsaron Najeriya Ta Karyata Bayanan Amurka kan Kisan Abu Bilal Al Minuki
- Hedikwatar tsaro ta yi karin haske game da rahotanni kan kisan hatsabibin dan ta'adda, Abu Bilal Al-Minuki da aka yi
- Rundunar ta bayyana gaskiya kan rawar kasar Amurka da ta ke ikirarin ta hannunta aka kashe kashe shugaban ISIS Abu Bilal Al-Minuki
- Janar Michael Onoja ya ce Amurka ta bayar da tallafin bayanan sirri, sa ido da bincike kawai, ba tare da tura sojojinta ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Hedikwatar tsaron Najeriya ta kalubalanci bayanai daga Amurka kan kisan shugaban ISIS, Abu Bilal Al-Minuki.
Rundunar ta bayyana cewa babu wani sojan ƙasashen waje da ya shiga farmakin ƙasa da ya hallaka shugaban ‘yan ta’addar ISIS. Daraktan yaɗa labaran harkokin tsaro, Manjo Janar Michael Onoja, ne ya bayyana hakan yayin wata hira da aka yi da shi a talabijin, cewar Punch.

Kara karanta wannan
Tinubu ya yi magana bayan Amurka ta yi ikirarin kashe kasurgumin dan ta'adda a Najeriya
Onoja ya ce ƙasar Amurka ta taimaka ne kawai da bayanan sirri, sa ido da bincike, tare da wasu kayan tallafin aiki.
Ya jaddada cewa babu wani sojan ƙasar waje da ya taka ƙasa yayin gudanar da farmakin da ya kai ga kashe Al-Minuki.
Ya bayyana aikin a matsayin farmaki na musamman da aka tsara cikin hikima domin hallaka babban ɗan ta’adda mai muhimmanci.
A cewarsa, farmakin ya nuna ƙwarewa, ladabi da cikakken shirin da sojojin Najeriya suka nuna yayin aikin.
Onoja ya ce babu wani soja da ya rasa ransa daga ɓangaren dakarun Najeriya saboda ƙwarewar jami’an da suka gudanar da aikin. Ya ce an tsara farmakin ne bayan tattara sahihan bayanan sirri da haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro.
Ya kuma bayyana cewa rahotannin da suka ce an kashe Al-Minuki tun shekarar 2024 sun samo asali ne daga kuskuren tantance mutum.
Ya ce Al-Minuki na amfani da sunaye daban-daban domin kaucewa gano shi tsawon shekaru.
A cewarsa, sunan Al-Minuki ya daɗe yana cikin jerin masu sa ido na ƙasashen duniya da hukumomi irin su Majalisar Ɗinkin Duniya da Amurka da Tarayyar Turai da Najeriya.
Ya ce watanni da dama aka shafe ana bibiyar bayanai kafin gano inda yake.
Onoja ya ce jami’an tsaro sun ƙaddamar da farmakin ne bayan tabbatar da sahihan bayanai kan inda shugaban ‘yan ta’addan yake.
Ya ƙara da cewa Najeriya za ta ci gaba da ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro da ƙasashen duniya wajen yaƙi da ta’addanci.
Daraktan ya kuma bayyana cewa har yanzu ana bibiyar wasu manyan ‘yan bindiga da masu tayar da ƙayar baya, ciki har da Bello Turji.
Ya ce Turji ba zai iya ɓuya har abada ba, domin lokaci ne kawai ya rage kafin a kamo shi.
Onoja ya buƙaci ‘yan Najeriya su ci gaba da bai wa jami’an tsaro bayanai cikin lokaci domin taimakawa ayyukan tsaro.
Ya kuma yi gargaɗin cewa biyan kuɗin fansa yana ƙarfafa ayyukan masu laifi tare da tsawaita matsalar rashin tsaro a ƙasa.
Asali: Legit.ng
