Eid al-Adha: Kasar Saudiyya Ta Sanar da Ranakun Hawan Arafah da Babbar Sallah

Eid al-Adha: Kasar Saudiyya Ta Sanar da Ranakun Hawan Arafah da Babbar Sallah

Saudi Arabia - Kasar Saudiyya ta tabbatar da cewa an ga jinjirin watan Zul-Hijja a yau Lahadi, 29 ga watan Zul Ka'ada, 1447AH wanda ya zo daidai da 17 ga watan Mayu, 2026.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sakamakon haka, gwamnatin Saudiyya ta ayyana gobe Litinin, 18 ga watan Mayu, 2026 a matsayin 1 ga watan Zul-Hijja, wata na 12 a kalandar watannin addinin musulunci.

Wata.
Yadda na'ura ta hasko jinjirin wata a sararin samaniya Hoto: @Haramaininfo
Source: Twitter

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da masarautar Saudiyya ta fitar kuma aka wallafa ta a shafin hukumar kula da masallatai masu alfarma na Makkah da Madinah na manhajar X.

Sanarwar ta bayyana cewa sakamakon shigar watan Zul Hijja a gobe Lahadi, za a yi hawan Arafah a ranar Talata, 9 ga watan Zul-Hijja, 1447AH daidai da 26 ga watan Mayu, 2026.

Haka zalika Saudiyya ta ayyana ranar Laraba, 27 ga watan Mayu, 2026 a matsayin ranar babbar Sallah (Eid el-Adha) wacce ake yi washe harin Arafah, 10 ga Zul-Hijjah.

Kara karanta wannan

Allah ya kawo mu, Sarkin Musulmi ya fitar da sanarwa kan ranar babbar Sallah a Najeriya

Sanarwar ta ce:

"An ga jinjirin wata na Zul Hijjah 1447 a Saudiyya. Sakamakon haka, watan Zul Hijjah mai albarka zai fara a daren yau, kuma za a yi bikin babar sallah, Eid al-Adha a ranar Laraba 27 ga Mayu 2026, in sha Allah."

Saudiyya ta kuma yi wa musulman da duka je kasar aikin Hajji fatan yin ibada karbabba, tare da addu'ar Allah Ya mayar da kowanensu gida lafiya.

"Allah SWT Ya ba wa masu aikin Hajji damar kammala wannan ibada lafiya, kuma karbabba, ya sauƙaƙa musu kowane mataki na tafiyarsu, Ya kuma gafarta masu, Ya mayar da su gida kamar ranar da aka haife su.
"Muna rokonnAllah Ya kuma ba mu damar dagewa a kwanaki goma na farko na Zul Hijjah wajen zikiri, azumi, addu'a, sadaka da ayyukan alheri, Ya kuma karɓi dukkan ibadunmu da ƙoƙarinmu," in ji sanarwar.

A wani labarin, kun ji cewa

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262