Bayanai Sun Fito: An Gano dalilin Tinubu na Yi wa Ribadu 'Kishiya' a Harkar Tsaro

Bayanai Sun Fito: An Gano dalilin Tinubu na Yi wa Ribadu 'Kishiya' a Harkar Tsaro

  • Bayanai na ci gaba da fitowa game da matakin Bola Tinubu na nadin sabon mai ba shi shawara kan tsaron cikin gida a Najeriya
  • Rahotanni sun nuna cewa nadin na da alaka da rashin jituwar jami’an tsaro da mai ba shugaban kasa shawara, Nuhu Ribadu
  • Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa sabon nadin zai taimaka wajen karfafa hadin gwiwar hukumomin tsaro da kawo sabuwar hanya wajen magance matsalar tsaro

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Rahotanni sun bayyana cewa nadin sabon mai bai wa shugaban kasa shawara kan tsaron cikin gida ya samo asali ne daga matsin lamba na jami’an tsaro.

Majiyoyi daga fadar shugaban kasa sun ce shugabannin sojoji da jami’an leken asiri sun nuna rashin jin dadinsu da yadda NSA, Nuhu Ribadu ke gudanar da aiki.

Kara karanta wannan

Yahudawa sun bankawa masallaci, motoci wuta yayin ibada a Isra'ila

An gano dalilin yi wa Ribadu 'kishiya' a Najeriya
Mai ba shugaban kasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu da Bola Tinubu. Hoto: Nuhu Ribadu, Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Twitter

Dalilin nada Famadewa a ofishin tsaron cikin gida

Wata majiya ta fadawa Punch cewa shugabannin tsaro sun zargi Ribadu da shiga harkokin gudanar da ayyukan soja maimakon takaitawa wajen bai wa shugaban kasa shawara.

Majiyar ta bayyana cewa an fara ganin wani sabon tsari inda ake amfani da tawagar Nuhu Ribadu wajen gudanar da wasu ayyukan tsaro a fili.

A ranar 11 ga Mayu, 2026 shugaba Bola Tinubu ya amince da nadin Manjo Janar Adeyinka Fadewa mai ritaya a matsayin mai ba shi shawara.

Sanarwar da gwamnatin tarayya ta fitar ta ce nadin Fadewa zai taimaka wajen karfafa hadin gwiwar hukumomin tsaro da inganta tattara bayanan sirri.

Rahotanni sun ce shugaban kasa yana neman sabuwar hanya domin samun cikakken bayani kan matsalar tsaro da kuma kawo karshen rikicin shekaru masu yawa.

Wata majiya ta bayyana cewa gwamnati na kashe makudan kudade wajen yaki da matsalar tsaro maimakon amfani da kudin wajen inganta ilimi da hanyoyi.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya yi sabon nadin mukami da zai taba rayuwar matan Najeriya

An nada mai ba da shawara kan tsaron cikin gida
Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Manjo Janar Adeyinka A. Famadewa (mai ritaya). Hoto: @aonanuga1956.
Source: Twitter

Manufar nadin Famadewa domin taimakawa tsaro

Fadar shugaban kasa ta ce sabon mai bai wa shugaban kasa shawara da NSA Ribadu za su yi aiki tare domin samar da ingantaccen tsaro ga ’yan Najeriya.

Shugaba Tinubu ya buƙaci Janar Famadewa da ya yi amfani da dukkan kwarewarsa da kishin ƙasa wajen ganin an cimma muradun tsaron Najeriya.

Manufar wannan naɗi ita ce tabbatar da cewa hukumomin tsaro sun haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen gano barazana tun kafin ta auku ta hanyar amfani da fasahar zamani da leken asiri.

Wannan mataki dai na zuwa ne a lokacin da Najeriya ke fuskantar ƙalubale daban-daban na tsaro wanda ke jawo matsaloli a kasar, cewar Leadership.

Ribadu ya gana da mataimakin Trump a Amurka

Mun ba ku labarin cewa mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ya tattauna batun yaki da ta'addanci tare da mataimakin shugaban Amurka.

Kara karanta wannan

Sulhu ko kato bayan kato: Jam'iyyar APC ta kaddamar da fara zaben fitar da gwani

Gwamnatocin Najeriya da Amurka sun ƙarfafa haɗin gwiwa wajen musayar bayanan sirri da kuma haɗin kan soja domin yaƙar Boko Haram da sauransu.

Shugaba kasa Bola Tinubu ya nuna godiya bisa ci gaba da tallafin horaswa da bayanan sirri da gwamnatin Amurka ke bai wa jami’an tsaron Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.