NJC Ta Saurari Koke Koke kan Alkalai 256, Ta Ladabtar da Wasu daga Cikinsu

NJC Ta Saurari Koke Koke kan Alkalai 256, Ta Ladabtar da Wasu daga Cikinsu

  • Hukumar shari'a ta kasa (NJC) ta ba wa Shugaba Bola Tinubu shawarar naɗa sababbin alkalan kotun daukaka kara guda 12
  • An aikawa alkalai 256 takardar tambaya kan batutuwan da suka shafi gudanar da aiki, tare da korar wasu da kakaba masu takunkumai masu tsanani
  • Hukumar ta yabi alkalai masu ƙwazo tare da jaddada gyare-gyaren da suka shafi riƙon amana da bayyana gaskiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Hukumar Shari'a ta Ƙasa (NJC) ta ba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu shawarar naɗa sababbin alkalan kotun daukaka kara guda 12.

Hukumar NJC ta kuma dauki tsauraran matakan ladabtarwa da suka shafi jami'an shari'a a faɗin ƙasar.

Hukumar NJC ta ladabtar da wasu alkalai
Alkalin alkalai ta Najeriya, Kudirat Kekere-Ekun Hoto: @njcNig
Source: Facebook

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da hukumar ta sanya a shafinta na X a ranar Alhamis, 14 ga watan Mayun 2027.

Kara karanta wannan

NDC: Jam'iyyar su Kwankwaso ta fitar da kudin fom din takarar 2027

Hukumar ta kuma aikawa alkalai 256 takardar tambaya kan abin da ta siffanta da "batutuwa daban-daban da suka shafi gudanar da aiki", biyo bayan taron ta na 111 da ta gudanar a ranar Laraba, 13 ga watan Mayu.

NJC ta duba daruruwan koke-koke

Sanarwar wadda mataimakiyar daraktan yaɗa Labarai, Kemi Babalola-Ogedengbe ta sanya wa hannu, NJC ta ce ta yi nazari kan koke-koke guda 98 da aka gabatar.

A cewar hukumar, an yi watsi da yawancin koke-koken, yayin da wasu kuma suka haifar da gargaɗi, bincike, da sauran matakan ladabtarwa.

NJC ta bayyana cewa an yi watsi da koke-koke guda 68 saboda rashin hujjoji, yayin da aka gargaɗi alkalai huɗu, sannan aka ba wa alkali ɗaya gargaɗi na ƙarshe.

Ta ƙara da cewa an ba da shawarar a gudanar da ƙarin bincike kan koke-koke guda 11 da aka gabatar gaban kwamitin bincike.

Haka kuma ta bayyana cewa an dakatar da sauraron wasu korafe-korafen saboda tuni suna gaban kotuna.

An yabi jami'an shari'a saboda ƙwazo

Duk da matakan ladabtarwar, hukumar NJC ta kuma yabawa wasu alkalai masu ƙwazo a yayin gudanar da aikinsu.

Ta yabi alkalai tara saboda nuna abin koyi wajen ƙwazo, sannan ta amince da ba su takardun yabo ga waɗanda suka yanke hukunce-hukunce da aka duba sama da guda 21 a cikin lokacin da aka yi nazarin.

Kara karanta wannan

Sabani ya bulla APC bayan kifar da mutum 150 yayin tantance masu son takara

Hukumar NJC ta hukunta wasu alkalai
Mai shari'a Kudirat Kekere-Ekun, alkalin alkalai ta Najeriya Hoto: @njcNig
Source: Twitter

An dakatar da alkalai 2

NJC ta tabbatar da dakatar da alkalai biyu na tsawon shekara guda ba tare da albashi ba, sakamakon wasu shari'o'i daban-daban na zargin nuna halayyar da ba ta dace ba a aikin shari'a.

Ɗaya daga cikinsu, Hon. Justice Ibrahim D. Shekarau na babbar kotun jihar Nasarawa, an hukunta shi ne kan zargin karya dokokin gudanar da shari'a wajen bayar da umarni a wani al'amari na takaddamar kuɗi.

Hakazalika, an dakatar da Hon. Justice Edward A. E. Okpe na babbar kotun babban birnin tarayya Abuja saboda zargin yin adalci a wata shari'ar aure.

NJC ta fara bincike kan alkalai

A wani labarin kuma, kun ji cewa hukumar shari’a ta kasa (NJC) ta ƙaddamar da wani bincike na sirri kan wasu manyan alkalai a kasar nan.

Binciken dai da hukumar NJC ta fara ya shafi har da shugabannin kotuna, bayan samun korafe-korafe da dama a kansu.

Majiyoyin sun bayyana cewa binciken na musamman ya biyo bayan ɗimbin korafe-korafe da aka shigar kan wasu “manyan jami’an shari’a” waɗanda ba a ambaci sunayensu ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng