Sauki Ya Samu: Gwannatin Tinubu Ta Kaddamar da Motocin CNG da na Lantarki a Kano

Sauki Ya Samu: Gwannatin Tinubu Ta Kaddamar da Motocin CNG da na Lantarki a Kano

  • Gwamnatin tarayya ta fara aiwatar da shirin motocin CNG da na lantarki a Kano domin rage kuɗin sufuri da bunƙasa amfani da makamashi mai tsafta
  • Gwamna Abba Yusuf ya ce shirin zai taimaka wajen sauƙaƙa zirga-zirga, rage wahalar man fetur da kare muhalli a jihar Kano
  • Hukumar PI-CNG & EV ta bayyana cewa an horar da sama da ‘yan Najeriya 7,000 tare da kafa cibiyoyin gyaran CNG 41 a sassan jihar Kano

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Kano - An ƙaddamar da shirin gwamnatin tarayya na motocin CNG da na lantarki a jihar Kano, wani mataki da ake ganin zai taimaka wajen rage kuɗin sufuri da bunƙasa amfani da makamashi mai tsafta a Najeriya.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ne ya ƙaddamar da shirin ranar Alhamis, inda ya ce wannan na daga cikin ƙoƙarin tallafa wa manufofin gwamnatin tarayya na amfani da makamashi na zamani a harkokin sufuri.

Kara karanta wannan

An cafke dan bindiga da ya je zai karbi miliyoyin kudin fansa

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da motocin CNG da na lantarki a Kano
Wasu daga cikin motocin bas masu amfani da CNG da lantarki da aka kaddamar a Kano. Hoto: @KanoFirstMedia
Source: Twitter

An kaddamar da motocin CNG a Kano

Gwamnan ya ce gwamnatin Kano za ta ci gaba da samar da ingantaccen tsarin sufuri domin rage wahalar zirga-zirga da kuma rage kuɗin da jama’a ke kashewa wajen sufuri, in ji rahoton Arise News.

Ya kara da cewa shirin zai taimaka wajen kare muhalli da rage dogaro da man fetur da ake amfani da shi wajen tafiyar da ababen hawa.

Da yake jawabi a wajen taron, mai kula da shirin CNG na kasa, Barista Isma’il Ahmad, ya bayyana cewa wannan shiri na daga cikin manyan tsare-tsaren gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin sauya tsarin sufuri a Najeriya.

Ya ce gwamnatin Tinubu tana son samar da hanyoyin sufuri masu sauki da kuma amfani da makamashi mai tsafta domin rage radadin cire tallafin man fetur.

An kafa cibiyoyin gyaran CNG a Kano

Isma’il Ahmad ya bayyana cewa tun bayan fara shirin, hukumar PI-CNG & EV ta yi aiki tare da gwamnatocin jihohi, kamfanoni masu zaman kansu, cibiyoyin kuɗi da masu harkar sufuri domin bunƙasa tsarin amfani da gas wajen sufuri a Najeriya.

Kara karanta wannan

An saki sunayen kananan hukumomi 3 da Boko Haram ta tilasta wa biyan haraji a Yobe

Ya ce kawo yanzu an fara aiwatar da shirin gyaran motocin CNG a jihohi sama da 28 a Najeriya.

A cewarsa, an kuma samar da tashoshin sayar da gas sama da 58 tare da tura dubban bas-bas da adaidaita sahu masu amfani da CNG a manyan hanyoyin sufuri.

Ya kara da cewa Kano na da cibiyoyin gyaran motocin CNG guda 41 daga cikin sama da cibiyoyi 300 da aka kafa a Najeriya, in ji rahoton Punch.

An samar da motocin CNG da wuraren gyaransu yayin da aka horar da matasa kusan 7,000 a Kano.
Gwamna Abba Yusuf da Barista Ismail sun kaddamar da shirin motocin CNG da lantarki a Kano. Hoto: @KanoFirstMedia
Source: Twitter

An horar da matasa 7,000 kan harkokin CNG

Jami’in ya bayyana cewa sama da matasan Najeriya 7,000 aka horar kan harkokin CNG da motocin lantarki domin samar da ayyukan yi da bunkasa fasahar zamani a fannin sufuri.

Ya ce shirin zai taimaka wajen samar da sabbin damammaki ga matasa tare da rage tsadar sufuri da dogaro da man fetur.

Masu lura da al’amura sun bayyana cewa shirin motocin CNG da lantarki na iya taimakawa wajen rage tsadar rayuwa idan aka aiwatar da shi yadda ya kamata.

Matakan da Tinubu ya dauka kan CNG

Kara karanta wannan

Majalisar dinkin duniya ta sa baki kan harin sojojin sama da ya kashe farar hula a Zamfara

A wani labari, mun ruwaito cewa, shugaban kasa Bola Tinubu ya jagoranci taron majalisar zartarwa na kwanaki biyu, inda majalisar ta amince da ayyuka da tsare-tsare 20.

A cikin wadannan ayyuka da tsare-tsaren, akwai wadanda kacokan suka fito da kudurorin Tinubu na janye Najeriya daga dogara da fetur zuwa iskar gas.

Matakin farko da Tinubu ya dauka shi ne ba da umarnin cewa ma’aikatu da hukumomin gwamnati su koma sayo ababen hawa da ke amfani da iskar gas din CNG.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com