“N200/L”: Kamfanin Najeriya Ya Gina Gidajen Man CNG, Zai Karya Farashin Man Fetur

“N200/L”: Kamfanin Najeriya Ya Gina Gidajen Man CNG, Zai Karya Farashin Man Fetur

  • Kamfanin iskar Gas na NIPCO ya ce ya kammala aikin gina gidajen sayar da iskar gas din CNG guda hudu a Legas
  • Kamfanin ya bayyana cewa gidajen man za su fara zuba man CNG ga ababen hawa a jihar daga watan Afrilu
  • NIPCO ya ce zai rika siyar da CNG ga masu ababen hawa a kan N200/scm idan aka kwatanta da N670/L na man fetur

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kamfanin iskar gas na NIPCO ya kammala ginawa da kuma bude sabbin gidajen sayar da gas din CNG guda hudu a Legas domin karya farashin man fetur.

Za a bude gidajen man guda hudu domin ayyukan kasuwanci a karshen watan Afrilu kuma za su zama na farko a Legas.

Kara karanta wannan

Akwai dalili: Shekara 1 na Shugaba Tinubu ta fi shekaru 8 na mulkin Manjo Buhari, Reno Omokri

Wani kamfanin ya kammala gina gidajen gas din CNG a Legas
Kamfanin NIPCO ya sanar da bude sabbin gidajen siyar da gas din CNG guda hudu a Legas. Hoto: NurPhoto
Asali: Getty Images

CNG ya fi rahusa a kan fetur

A cewar Nagendra Verma, manajan kamfanin gas na NIPCO, kamfanin ya tsunduma cikin harkar kasuwancin gas tun daga 2009.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Leadership ta ruwaito cewa shugaban NIPCO ya bada tabbacin dorewar samar da iskar gas da kuma siyar da shi a kan N200 maimakon N670 da ake siyan man fetur a Abuja.

Verma ya ce ga manyan motoci, za su sayi CNG a kan N260/scm maimakon Naira 1,250 na dizal a Legas da kuma N290/scm na CNG sabanin N1,300 a kan kowace litar dizal a Abuja.

Verma ya ce:

"NIPCO Gas yana da tabbacin cewa la'akari da kokarin gwamnati mai ci na mayar da hankali kan AutoCNG, iskar za ta maye gurbin man fetur a Najeriya nan ba da dadewa ba."

NIPCO ya bude gidajen mai 15 a Najeriya

Kara karanta wannan

Bangaren maza ko mata? Hukumar Gidan Yari ta fadi sashen da za ta ajiye Bobrisky

Ya bayyana cewa CNG mai ne na talakawa kuma yana da mahimmanci ga kasa, yana mai cewa idan kamfanin ya fadada a Najeriya, zai rage masu ababen hawa tsadar man fetur.

Yayin bayyana dabarun kamfanin, jaridar The Guardian ta ruwaito shi yana cewa kamfanin ya fara ne a cikin garin Benin kafin ya fadada harkokinsa na CNG zuwa jihar Ogun da Kogi.

Kamfanin NIPCO yana aiki da tashoshin CNG guda 15 a fadin Najeriya, kuma motocin CNG a Legas na bin hanyar da ke tsakanin tashoshin kamfanin idan za su je Abuja da Kaduna.

IPMAN za ta fara dakon CNG

A wani labarin, Legit Hausa ta ruwaito cewa dillalan man fetur na Najeriya sun sanar da cewa suna daf da fara dako da kasuwancin iskar gas din CNG.

A cewar kungiyar, man CNG zai iya maye gurbin man fetur la'akari da cewa ya fi fetur arha kuma baya saurin konewa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel