‘Za a Fara Harbe Su’: Matakin Gwamnatin Plateau man Makiyaya Masu Lalata Gona
- Gwamnatin jihar Plateau ta shirya daukar mataki mai tsauri kan makiyaya masu lalata gonakin mutane domin dakile rikicin a yankuna
- Gwaman Caleb Mutfwang, ya ce zai bai wa jami’an tsaro umarnin harbe duk wanda aka kama yana lalata gonakin jama’a a fadin jihar
- Mutfwang ya bayyana cewa kashe mutane saboda satar ko kashe shanu rashin hankali ne, yana mai cewa babu rai da za a kwatanta da dukiyar dabbobi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Jos, Plateau - Gwamnan jihar Plateau, Caleb Mutfwang, ya koka game da yadda rikicin manoma da makiyaya ke jawo asarar rayuka.
Gwamnan ya bayyana cewa gwamnati za ta dauki tsauraran matakai kan masu lalata gonakin jama’a a fadin jihar.

Source: Facebook
Mutfwang ya bayyana cewa lokacin da ake kama masu irin wadannan laifuka ana kai su Abuja domin gudanar da bincike ya wuce gaba daya, cewar RFI Hausa.

Kara karanta wannan
"Babu hujja," Sojojin Najeriya sun yi magana kan zargin kashe fiye da mutane 100 a Zamfara
Ya ce zai bai wa jami’an tsaro umarnin harbe duk wanda aka kama yana barnata amfanin gona, domin kawo karshen rikice-rikicen da suka addabi yankin.
A cewarsa, babu wanda ya fi karfin doka, saboda haka duk wanda aka samu yana aikata irin wannan barna zai fuskanci hukunci mai tsauri.
Gwamnan ya kuma yi Allah wadai da kashe mutane saboda rikicin shanu, yana mai cewa babu wata dabba da ta kai darajar ran dan Adam.
Ya bukaci masu kiwo da sauran jama’a su rika sanar da hukumomi idan an sace musu shanu maimakon daukar doka a hannunsu.
Mutfwang ya ce hukumomi za su taimaka wajen nemo shanun da suka bace ko kuma lalubo hanyoyin biyan diyya idan hakan ta zama dole.
Ya kara da cewa lokaci ya yi da za a kawo karshen rashin tsaro da rikice-rikicen da suka dade suna haddasa tashin hankali a Filato.
Sai dai wasu mutane sun nuna damuwa cewa sabon matakin gwamnati zai iya cutar da wasu bangarori musamman Fulani makiyaya da ake kashewa shanunsu.
Masu sharhi kan harkokin tsaro na ganin cewa wajibi ne gwamnati ta tabbatar da adalci domin kauce wa kara ruruta rikicin da ke faruwa a jihar.
Karin bayani na tae...
Asali: Legit.ng