Fulani Makiyaya
Sojoji sun hana arangama tsakanin ƴan ƙabilar Fulani da Mwaghavul a karamar hukumar Mangu, Plateau, bayan musayar wuta kusa da kauyukan Gaude da Aloghom.
Ooni na Ife ya tallafa wa cibiyar tsaron Iru Ekun ta Sunday Igboho da Naira miliyan 100 da motar Hilux, tare da kira ga Yarbawa su hada kai wajen inganta tsaro.
Sarkin Musulmi ya ce Fulani ba masu laifi ba ne, ya bukaci a daina danganta garkuwa da mutane da su, tare da alkawarin haɗin gwiwa da jami'an tsaro.
Kotun tarayya ta ƙi sauraron buƙatar Bello Bodejo kan sauya sharudan beli, ta ce ya garzaya wajen alkalin hutun kotu yayin da shari'ar EFCC ke ci gaba.
An kashe makiyaya uku a jihar Filato bayan harin da aka kai musu a Riyom. Kungiyar MACBAN ta zargi matasan Berom, amma BYM ta musanta wannan zargin.
Shugaban Miyetti Allah Kautal Hore, Bello Bodejo, ya musanta tuhume-tuhume 12 da EFCC ta shigar masa kan zargin wanke kudade da daukar nauyin ta'addanci.
Wani ɗan sanda ya mutu, fararen hula uku suka ji rauni bayan harin wasu mahara a Gembu, yayin da karamar hukuma ta sanya dokar hana fita ta dare.
Gwamnatin jihar Neja karkashin jagorancin Gwamna Umaru Bago ta sanya dokar hana fita a wasu garuruwa biyo bayan barkewar rikicin kabilanci da ya jawo asarar rayuka.
A labarin nan, za a ji cewa wata saniya ta jawo rikici a tsakanin manoma na makiyaya a jihar Kano, lamarin da ya jawo aka gwabza har mutum 12 suka jikkata.
Fulani Makiyaya
Samu kari