Yadda Aka Tatsi Bayanai daga Wadanda Ake Zargi da Shirya Juyin Mulkin Tinubu
- Ana ci gaba da shari'ar game da da zargin hannun wasu a yunkurin juyin mulki a gwamnatin Bola Tinubu
- Wata shaidar gwamnati ta fada wa kotun tarayya da ke Abuja cewa wadanda ake zargi sun bayar da bayanansu bisa ka'ida
- Lauyoyin wadanda ake kara sun dage cewa an karbi bayanan ne cikin matsin lamba, yayin da kotu ta ci gaba da sauraron karar
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Wata shaidar gwamnati ta bayyana wa Babbar Kotun Tarayya yadda ake tatsar bayanai game da zargin wasu da hannu a yunkurin juyin mulki.
Shaidar ta bayyana cewa mutane shida da ake zargi da yunkurin juyin mulki sun bayar da bayanansu cikin son rai.

Source: Facebook
Shari’ar ta shafi zargin shirya hambarar da gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, bayan bayanan sirri sun isa hannun hukumomi a watan Satumban bara, cewar Premium Times.

Kara karanta wannan
Kotu ta yanke hukunci, ta ci tarar wanda ya nemi a rushe babban taron APC na kasa
Juyin mulki: Ana zargin tatsar bayanai bisa tilas
Mai shari’a, Joyce Abdulmalik, ta dakatar da sauraron karar domin gudanar da shari’a cikin shari’a kan sahihancin bayanan da aka karba daga wadanda ake tuhuma.
Lauyoyin wadanda ake kara sun yi zargin cewa an karbi bayanan ne ta hanyar matsin lamba da tilastawa yayin binciken da jami’an tsaro suka gudanar.
Sai dai lauyan gwamnatin tarayya, Rotimi Oyedepo, ya ce gwamnati na da shaidu uku da za su tabbatar da cewa an bi ka’idojin doka wajen binciken.
Shaidar farko mai lakabin AAA saboda dalilan tsaro ta bayyana cewa an dauki bidiyon dukkan zaman tambayoyin da aka yi wa wadanda ake zargi.
Shaidar ta ce wadanda ake tuhuma sun kasance cikin natsuwa kuma sun san hakkokinsu na kundin tsarin mulki kafin bayar da bayanansu ga jami’an bincike.
Wadanda ake tuhuma da zargin juyin mulki
Daga cikin wadanda ake kara akwai tsohon janar, Mohammed Ibrahim Gana, tsohon jami’in ruwa, Erasmus Ochegobia Victor, da sufeton ’yan sanda, Ahmed Ibrahim.
Sauran sun hada da Zekeri Umoru, Bukar Kashim Goni da malamin addini, Abdulkadir Sani Khalifa da ke zaune a Zariya.
An tuhume su da laifuka 13 da suka hada da cin amanar kasa, ta’addanci, boye bayanai da kuma wanke kudade kan yunkurin juyin mulkin da ake zargi.
Shaidar ta ce babu wani daga cikin wadanda ake zargi da aka hana damar samun lauya, duk da cewa babu lauyoyi a lokacin daukar bayanansu.
Ta kuma bayyana cewa an samar da mai fassara daga Hausa zuwa Turanci ga daya daga cikin wadanda ake tuhuma saboda rashin iya Turanci sosai, cewar Punch.
Kotun ta dage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 13 ga watan Mayu domin ci gaba da tantance ko an bayar da bayanan cikin son rai ko akasin haka.
Juyin mulki: Sheikh Khalifa ya magantu a kotu
Mun ba ku labarin cewa babban malamin musulunci a Zaria, Sheikh Sani Khalifa ya gabatar da bayani kan zargin da ake yi masa na hannu a shirin juyin mulki.
Bayanin malamin na cikin wani faifan bidiyo da bangaren gwamnatin tarayya ya gabatar a zaman babbar kotun tarayya.
Malamin ya tabbatar da cewa an tuntube shi domin ya yi addu'a ga masu shirin juyin mulki, amma ya gargade su da cewa ba za su yi nasara ba.
Asali: Legit.ng

