Kwankwaso Ya Hakura, Ya Shirya Goyon Bayan Peter Obi ko Wani 'Dan Takara a Zaben 2027
- Tsohon 'dan takarar shugaban kasa, Sanata Rabiu Kwankwaso ya ce zai goyi bayan duk wanda NDC ta tsayar takara a zaben 2027
- Hakan na zuwa ne bayan jam’iyyar ta amince da mika tikitin shugaban kasa zuwa Kudancin Najeriya na wa’adi daya
- Kwankwaso ya ce yana iya zama mataimakin 'dan takarar da NDC za ta dauko daga Kudu idan jam’iyya ta yanke shawarar hakan
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria - Tsohon dan takarar shugaban kasa, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa a shirye yake ya mara wa duk dan takarar da jam’iyyar NDC ta tsayar baya a zaben 2027.
Kwankwaso ya yi wannan furuci ne kwanaki kadam bayan ya koma NDC tare da tsohon dan takarar shugaban kasa na LP, Peter Obi.

Source: Twitter
Tsohon gwamnan Kano ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi a shirin PrimeTime na gidan talabijin na Arise TV.

Kara karanta wannan
Jonathan ya amsa kiran 'yan Najeriya, zai tsaya takarar shugaban kasa a jam'iyyar PDP
Kwankwaso zai yi takara a 2027?
Jagoran Kwankwasiyya ya ce NDC ta cimma matsayar mika takara yankin Kudu ne bayan tattaunawa da shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki daga sassan kasar nan.
“Idan jam’iyya ta yanke shawarar in zama abokin takarar wani daga Kudu, a shirye nake na amince da hakan."
“Tun daga farko mun zauna muka duba halin da kasar nan ke ciki, sannan muka dauki manyan matakai ciki har da mika tikitin shugaban kasa zuwa Kudu na shekaru hudu, bayan haka mulkin zai dawo Arewa.”
Dalilin mika tikitin takara zuwa Kudu
Kwankwaso ya ce ‘yan Arewa da suka shiga jam’iyyar NDC sun amince da tsarin ne saboda suna ganin hakan zai taimaka wajen kawo karshen rikicin tsarin karba-karba, wanda ya biyo bayan rasuwar tsohon shugaban kasa Umaru Musa Yar’Adua.
“Muna ganin mafi dacewa shi ne a kai mulkin zuwa Kudu domin kawo karshen rudanin da ya biyo bayan rasuwar shugaban kasa Umaru Musa Yar’Adua.
“Abin da ya fi muhimmanci yanzu ba Arewa ko Kudu ba ne, illa samun shugabanci nagari daga mutane masu himma da kishin kawo cigaba ga kasa,” in ji shi.

Source: Facebook
Kwankwaso da Obi sun tattauna kan tsaro
Tsohon gwamnan ya kuma bayyana cewa shi da Peter Obi sun tattauna hanyoyin magance matsalar tsaro musamman a Arewacin Najeriya, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.
“Ni da Peter Obi mun tattauna hanyoyi da dama na yaki da rashin tsaro. Na yi aiki tare da mutane daga kowane bangare kuma na san ina da kwarewar da za ta taimaka,” ya ce.
Dalilin Kwankwaso na ficewa daga ADC
A baya, an ji cewa Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya ce matsalolin da suka jawo ficewarsa daga ADC kusan iri daya ne da wanda ya jawo ya bar NNPP.
Ya bayyana hakan ne kwanaki bayan sauya shekarsa daga haɗakar yan adawa, ADC zuwa sabuwar tafiya ta NDC wadda ke ci gaba da jan hankali a siyasar Najeriya.
Kwankwaso ya ce sun gano cewa an shiga wani yanayi da ake ƙoƙarin durkusar da rajistar jam’iyyar ADC ta hanyar shari’a.
Asali: Legit.ng
