Yadda 'Yan Sandan Najeriya Suka Ki Karbar Cin Hancin N100m

Yadda 'Yan Sandan Najeriya Suka Ki Karbar Cin Hancin N100m

  • Jami'an rundunar 'yan sandan Najeriya sun samu nasarar cafke wasu bata-gari da ke fasakwaurin kayayyakin layin dogo
  • An cafke mutanen ne lokacin da suke kan hanyar kai kayayyakin da suka sato zuwa jihar Kwara a yankin Arewa ta Tsakiya
  • A yayin bincike, an yi wa jami'an 'yan sanda tayin cin hancin N100m domin su saki kayan tare da mutanen da suka cafke

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT, Abuja - Jami'an rundunar ’yan sandan Najeriya (NPF) na sashen binciken sirri na musamman (FID-STS), sun ki karbar cin hancin Naira miliyan 100.

Jami'an 'yan sandan sun ki karbar cin hancin ne da wata ƙungiyar masu fasa ƙaurin kayan gwamnati suka yi ƙoƙarin ba su.

'Yan sanda sun ki karbar cin hanci
Sufeto Janar na 'yan sandan Najeriya, Olatunji Rilwan Disu Hoto: @PoliceNG
Source: Twitter

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar 'yan sanda, DCP Anthony Placid, ya sanya a shafin X a ranar Litinin, 27 ga watan Afirilun 2026.

Kara karanta wannan

'Yan ta'adda sun yi aika aika a Adamawa, Gwamna Fintiri ya sha alwashi

'Yan sanda sun cafke masu aikata laifi

Rundunar 'yan sandan ta samu gagarumar nasara wajen kama mutane biyu da ake zargi da yin barna mai yawa ga muhimman ababen more rayuwa na ƙasa tare da ƙwato kayan layin dogo da darajarsu ta haura N400,000,000.

Waɗanda ake zargin, Chisom Goodnews (ɗan shekara 32) da Ahmed Adamu (ɗan shekara 22), an kama su ne a ranar 9 ga Afrilu, 2026, da misalin ƙarfe 6:00 na yamma a garin Akwanga da ke jihar Nasarawa, biyo bayan bayanan sirri masu tushe.

DCP Anthony Okon Placid ya ce samamen ya kai ga kama wata babbar mota (tirela) maƙare da kusan tan 60 na kayayyakin layin dogo da aka sato.

Ya bayyana cewa an ɓoye kayayyakin ne a ƙarƙashin buhunan bawon gyaɗa da nufin kauce wa jami’an tsaro yayin da ake jigilar su daga jihar Bauchi zuwa birnin Ilorin na jihar Kwara.

'Yan sanda sun ki karbar cin hanci

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun hallaka malamin addini da iyalansa a Plateau

“Binciken farko ya nuna cewa an yi yarjejeniyar biyan direban motar N2.5m domin jigilar kayan da aka sato, yayin da ƙarin bincike ya nuna cewa akwai wani tsari na masu sato kayan da masu karɓa waɗanda ke da alaƙa da juna."
“Yayin gudanar da bincike, jami’an da suka gudanar da samamen sun yi watsi da tayin N100m da aka yi musu da nufin lalata binciken da kuma sakin waɗanda ake zargi tare da kayan da aka kama."

- DCP Anthony Placid

Ya ƙara da cewa an ƙwato babbar motar da aka yi amfani da ita wajen jigilar kayan, kuma ana ci gaba da bincike don kamo sauran mambobin ƙungiyar, ciki har da masu karɓar kayan, da kuma gano wasu ƙarin kayayyakin.

'Yan sanda sun kama kayan laifi
Jami'an 'yan sanda na duba motar da ke dauke da kayan laifin Hoto: @PoliceNG
Source: Twitter

An yaba wa jami'an 'yan sanda

“Sufeto Janar na ’yan sanda, IGP Olatunji Rilwan Disu, psc(+), NPM, ya yaba wa jami’an saboda jajircewarsu, tarbiyya, da kuma ƙin karɓar cin hanci, inda ya lura cewa irin waɗannan ayyuka su ne ainihin dabi’un rundunar."
“Rundunar ’Yan Sandan Najeriya za ta ci gaba da jajircewa wajen kare kadarorin ƙasa daga masu fasa ƙauri."

- DCP Anthony Placid

'Yan sanda sun cafke masu leken asiri

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun bude wuta kan bayin Allah a Katsina, an samu asarar rayuka

A wani labarin kuma, kun ji cewa jami'an 'yan sanda a Sokoto sun cafke wasu da ake zargi da ba ‘yan bindiga bayanai da kuma taimaka masu wajen samun kudade.

Kwamishinan ‘yan sanda na Sokoto, Hayatu Hassan Shaffa, ya ce jami’an sashen yaki da garkuwa da mutane sun kama wani Aminu Mai Roba daga kauyen Maikulki da ke karamar hukumar Binji.

Bincike ya nuna cewa wanda ake zargin ya amsa cewa ya karbi shanun ne daga kungiyar ‘yan ta’adda ta Lakurawa a kauyen Wariya da ke Tangaza.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng