" Za a Gama Titin Abuja Zuwa Kaduna Zuwa Katsina" Ministan Tinubu Ya Tsaida Lokaci

" Za a Gama Titin Abuja Zuwa Kaduna Zuwa Katsina" Ministan Tinubu Ya Tsaida Lokaci

  • Gwamnatin tarayya ta ce za ta kammala aikin gina titin Abuja-Kaduna-Kano-Katsina nan da karshen shekarar 2025
  • Ministan ayyuka, David Umahi wanda ya bayyana hakan ya ce kamfanin Dangote, BUA da Julius Berger ne za su yi aikin
  • Umahi ya ba da tabbacin kammala aikin titin Sokoto zuwa Badagry a kan lokaci wanda zai hada Kudu maso Gabas da Arewa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Ministan ayyuka David Umahi ya bayyana cewa gwamnatin tarayya na shirin kammala aikin hanyar Abuja-Kaduna-Kano-Katsina nan da shekarar 2025.

David Umahi ya ce shugaba Bola Tinubu ya umarce shi da ya samar da wani tsari da zai taimaka wajen kammala aikin titin a shekara mai zuwa.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Kano ta musanta shirin korar wadanda Ganduje ya dauka aiki

Gwamnati ta yi magana kan aikin titin Abuja-Kaduna-Katsina
Gwamnati ta dauki matakan kammala titin Abuja-Kaduna-Katsina zuwa 2025. Hoto: @FMWNIG
Asali: Twitter

Yadda za a gina titin Abuja-Katsina

Jaridar The Punch ta ruwaito Umahi, a wata ziyara da gwamnan Kaduna, Uba Sani, ya kai masa, ya yi bayani kan dabarun da ake aiwatarwa domin kammala aikin titin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A wata sanarwa da ya fitar a daren Laraba ta hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Uchenna Orji, ministan ya ce:

“Za a fara kammala kashi na farko na titin mai tsayi kilomita 76, wanda rukunin kamfanoni na Dangote ke aikin wanda zai gina shi da kankare.
"Za mu ba da izinin gina kilomita 82 na gaba ga kamfanin Julius Berger. Sannan kuma kamfanin BUA zai yi aikin kilomita 40 na ƙarshe wanda shi ma za a yi shi da kankare."

Gwamnati ta himmatu kan titin Sokoto-Badagry

Ministan ya kuma jaddada kudirin Shugaba Bola Tinubu na gudanar da aikin titin Sokoto zuwa Badagry cikin gaggawa tare da kammala shi a kan lokaci, jaridar Tribune ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Abba Gida-Gida ya kaddamar da titi mai hawa 3 a kan kudi ₦15bn a Dan Agundi

"Ma'aikatar ayyuka ta tarayya ce ke gudanar da aikin gina babbar hanyar kuma aikin zai shafi tsohuwar hanyar kasuwanci ta Afirka da ta bi ta Sokoto, Kebbi, Niger, Kwara, Ondo, Oyo, Ogun, Legas, ta kuma hade da Badagry."

- David Umahi

Ya ce ana shirin hada Kudu maso Gabas da Arewa ta hanyar gina titin kasuwancin wanda zai bi ta jihohin Binuwai, Kogi, Nasarawa, da kuma Abuja.

Gwamnati za ta kara harajin VAT

A wani labarin, Legit Hausa ta ruwaito gwamnatin tarayya ta ce akwai bukatar ta kara harajin VAT da take caja yayin da aka sayi kaya ko aka sayar.

Kwamitin shugaban kasa kan manufofin kasafin kudi da sauye-sauyen haraji ya kawo wannan shawar yana mai cewa hakan zai bunkasa tattalin arziki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.