‘Yan Siyasa da Sojojin da Aka Kashe a Juyin Mulkin Farko da Aka Yi a Junairun 1966

‘Yan Siyasa da Sojojin da Aka Kashe a Juyin Mulkin Farko da Aka Yi a Junairun 1966

  • A ranar 15 ga Junairu a shekarar 1966, sojoji suka fara hambarar da gwamnatin farar hula
  • Juyin mulkin ne ya yi sanadiyyar mutuwar manyan yankin Arewa irinsu Ahmadu Bello
  • Firayim Minista da wasu manyan sojojin Arewa sun hallaka a sanadiyyar juyin mulkin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Abuja - A ranar 15 ga watan Junairu a 1966, sojojin tawaye suka kifar da gwamnatin farar hula a karon farko a tarihin Najeriya.

Masana tarihi sun ce wannan bakin juyin-mulki ya jawo munanan abubuwan da suka biyo baya a kasar har zuwa yakin basasa.

Ahmadu Bello da Tafawa-Balewa
Ahmadu Bello da Tafawa-Balewa sun mutu a 1966 Hoto: Getty Images, AYCOMEDIAN
Asali: Getty Images

Sojojin da suka hambarar da gwamnatin Abubakar Tafawa Balewa sun kashe mutane da yawa, rahoton nan ya jero su.

Kara karanta wannan

Mutane 6 da Suka Taimakawa Abba Kabir Yusuf Wajen Samun Nasarar Kotun Koli

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Su wanene aka kashe a 1966?

1. Abubakar Tafawa Balewa

A juyin mulkin ne aka rasa Firimiyan Arewa, Abubakar Tafawa Balewa a Legas. Wanda ya jagoranci juyin mulkin, Emmanuel Ifeajuna ya kashe shi.

2. Ahmadu Bello

Manjo Chukuma Nzeogwu ya kashe Sardaunan Sokoto, Ahmadu Bello a gidansa a garin Kaduna tare da mai dakinsa, direbansa, dogari da kuma wani.

3. Samuel Akintola

Firimiyan Yamma a lokacin, Samuel Akintola ya ji labarin juyin mulkin kuma ya sanar da Ahmadu Bello. Akintola ya yi fada da sojoji kafin su harbe shi.

4. Festus Okotie-Eboh

Festus Okotie-Eboh yana cikin wadanda aka kashe daga kudancin Najeriya, ministan kudin mutumin Itsekiri da sojoji suka zarga da satar dukiyar kasa.

5. Birgediya Samuel Ademulegun

A juyin mulkin nan ne sojojin tawaye suka kashe Birgediya Samuel Ademulegun da mai dakinsa, Latifat, saura kiris ya gano shirin kifar da gwamnati a Kaduna.

Kara karanta wannan

Jam’iyyun adawa sun cigaba da shirin hada kai domin yakar Tinubu da APC a 2027

6. Birgediya Zakariya Maimalari

Saura kiris Birgediya Zakariya Maimalari ya kubuta, sai ya ci karo da motar Ifeajuna wanda ya buda masa wuta, shi ne babban soja daga Arewa lokacin.

7. Kanal Kur Mohammed

Wani babban soja da ake ji da shi daga Arewa a lokacin shi ne Kanal Kur Mohammed. An yi garkuwa da sojan ne, daga baya sojojin suka buda masa wuta.

8. Kanal Ralph Shodeinde

Rahoton Nairaland ya ce babu tabbacin yadda Ralpha Shodeinde ya mutu. Laftanan Kanal din shi ne shugaban makarantar sojin NMTC da aka kashe shi.

9. Laftanan Kanal James Pam

Laftanan Kanal James Pam ya sanar da Janar Johnson Aguiyi-Ironsi da shirin juyin mulkin, shi ma har gida aka zo aka dauke shi, sai dai aka gano gawarsa.

10. Laftanan Kanal Arthur Unegbe

Chris Anuforo ya harbi Laftanan Kanal Arthur Unegbe, wasu sun ce an yi haka ne saboda gudun ya fallasa asirin

11. Laftanan Kanal Abogo Largema

Kara karanta wannan

Hadiman Atiku 5 da su ka juya masa baya, suka yi aiki da Gwamnati da APC

An yi rashin dace Laftanan Kanal Abogo Largema ya baro birnin Ibadan, yana otel a Ikoyi a ranar, kamar Kur Muhammad da Maimalari, Largema Kanuri ne.

Sauran wadanda aka kashe su ne:

12. Ahmed Ben Musa

13. Hafsatu Bello

14. Mrs Latifat Ademulegun

15. Zarumi Sardauna

16. Ahmed Pategi

17. Sajen Daramola Oyegoke

18. PC Yohana Garkawa

19. Lans Kofir Musa Nimzo

20. PC Akpan Anduka

21. PC Hagai Lai

22. Philip Lewande

Zaben 2027 a Najeriya

Muddin ya gaza canza fasalin kasa da kirkiro da 'yan sanda a jihohi, Reno Omokri ya ce za a koma goyon bayan Atiku Abubakar.

An ji labari Omokri ya ce idan Peter Obi ya shiga takara a 2027, za a yi irin na 2023 da APC tayi nasara a karkashin Bola Tinubu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel