Menene dalilin da yasa aka kashe Ahmadu Bello Sardauna?

Menene dalilin da yasa aka kashe Ahmadu Bello Sardauna?

A yau an kwashe sama da shekaru 52 da suka gabata kenan da bindige gamji dan kwarai, Firimiya na farko kuma daya tilo na yankin Arewacin Najeriya, Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato.

Sir Ahmadu Bello ya kwanta dama ne a ranar Juma’a, 15 ga watan Janairu cikin watan Azumi na shekarar 1966, shekau shidda da samun yanci, inda wasu kananan hafsoshin soji suka far masa a daren juma’an suka yi masa ruwan harsasai.

KU KARANTA: Makarfi ya tsallake rijiya da baya a wani mummunan hatsarin mota

Manjo Chukwuemeka Kaduna Nzeogwu, wanda ya jagoranci kai harin ya bayyana dalilansa na kashe Sardauna; da suka hada da girman kai, cin hanci da rashawa, son kai, da kokarin kaddamar da jihadi a Najeriya.

Menene dalilin da yasa aka kashe Ahmadu Bello Sardauna?
Ahmadu Bello Sardauna

Sai dai an tabbatar gaba daya wadannan dalilan daya dogara akansu duk shaci fadi ne, don kuwa ko bayan da aka kashe Sardauna, an tarar da Banki na binsa bashi ne ma, maganan son kai kuwa, ai a wancan lokaci kowane yankin kasar nan kokari take ta gina jama’anta da yankinta.

Wani na hannun daman Sardauna, Sheikh Abubakar Gumi ne da kansa ya fada ma Manjo Nzeogwu karya yake yi game da zargin Sardauna da yake na kokarin kaddamar da jihadi, inda Shehin Malamin ya fada masa Sardauna bai taba tara makamai a ko ina ba don shirin yaki.

Manya cikin wadanda aka hallaka a wannan rana, a cikin mutane 22, sun hada da Firai ministan Najeriya, Abubakar Tafawa Balewa, Firai ministan yankin yammacin kasar nan Samuel Akintola, janar Zakari Mai Malari, Ademulegun, Ahmad Ben Musa, Yakubu Pam, Largema, Kur Muhammad.

Ga jerin sunayen mutanen da aka hallaka nan:

Ahmadu Bello Sardauna

Abubakar Tafawa Balewa

Menene dalilin da yasa aka kashe Ahmadu Bello Sardauna?
Tafawa Balewa

Samuel Ladoke Akintola

Menene dalilin da yasa aka kashe Ahmadu Bello Sardauna?
Firai ministan Yammacin kasar nan, Akintola

Festus Okotie-Eboh ministan kudi

Shugaban hafsan Soji Birgediya Samuel Ademulegun da matarsa Latifat Ademulegun

Menene dalilin da yasa aka kashe Ahmadu Bello Sardauna?
Ministan kudi da shugaban hafsan Sojin kasar

Ahmed Ben Musa Maigadin Sardauna

Hafsatu Bello Uwargidar Sardauna

Zarumi, shima ma’aikaci a gidan Sardauna

Ahmed Pategi Direban Sardauna

Kanal Ralph Shodeinde

Birgediya Zakariya Maimalari

Kanal Kur Mohammed

Menene dalilin da yasa aka kashe Ahmadu Bello Sardauna?
Kanal Kur Muhammed da Zakari Mai Malari

Laftanar kanal Abogo Largema

Laftanar kanar James Pam

Menene dalilin da yasa aka kashe Ahmadu Bello Sardauna?
Largema da Yakubu Pam

Sauran sun hada da:

Laftanar kanar Arthur Unegbe

Sajan Daramola Oyegoke abikin aikin Nzeogwu, daga baya Nzeogwun da kansa ya kashe shi

Yohana Garkawa

Kofur Musa Nimzo

Akpan Anduka

Hagai Lai

Philip lewande

Idan mai karatu ya duba jerin mutanen nan, zai fahimci dukkanin mutanen da aka kashe abokanan Sardauna ne a siyasance ko a addininance, ko kuma yanki daya ya hada su.

Yanzu karanta jerin mutanen da suka shirya tare da zartar da kashe wadannan bayin Allah da na ambata a sama:

Manjo Kaduna Nzeogwu

Manjo Adewale Ademoyega

Manjo Emmanuel Ifeajuna

Manjo Timothy Onwuatuegwu

Manjo Chris Anuforo

Manjo Humphrey Chukwuka

Manjo Don Okafor

Kyaftin Ogbo Oji

Sai mu kara tambayar kawunan mu, wai menene dalilin kashe Ahmadu Sardauna da Abubakar Tafawa Balewa?

Kalli dakin da Ojukwu ya boye a yayin yakin basasan Najeriya, kamar yadda Legit.ng ta kawo muku:

Asali: Legit.ng

Online view pixel