Innalillahi: Tsohon Kwamishinan ’Yan Sanda a Najeriya Ya Riga Mu Gidan Gaskiya, Sifeta Ya Kadu

Innalillahi: Tsohon Kwamishinan ’Yan Sanda a Najeriya Ya Riga Mu Gidan Gaskiya, Sifeta Ya Kadu

  • Fatai Shittu, wanda ya yi kaurin suna lokacin da ya ke kwamishinan 'yan sanda a jihar Zamfara ya rasu a jiya Juma'a
  • Babban Sifetan 'yan sanda, Kayide Egbetokun a madadin rundunar 'yan sandan ya tura sakon ta'aziyya ga iyalansa
  • Marigayin kafin rasuwarshi ya yi aiki a jihohin Zamfara da Legas da Imo da Ebonyi da Ogun da Kebbi da sauransu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, kwararren editan siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Babban Sifetan 'yan sanda a Najeriya, Kayode Egbetokun ya nuna alhininsa bayan mutuwar Fatai Adio Shittu mai ritaya.

Egbetokun ya bayyana kaduwarsa ne a yau Asabar 18 ga watan Nuwamba na tsohon kwamishina 'yan sandan a Najeriya, Legit ta tattaro.

Tsohon kwamishinan 'yan sanda a Najeriya ya riga mu gidan gaskiya
Marigayi Shittu ya yi aiki a jihohi da dama a kasar. Hoto: NPF.
Asali: Facebook

Yaushe Shittu ya rasu?

Kara karanta wannan

Bayan tsige gwamnan Kano, Malamin addini ya yi hasashen sakamakon hukuncin zaben Kaduna da Nasarawa

Rahotanni sun tattaro cewa Shittu ya rasu ne a jiya Juma'a 17 ga watan Nuwamba ya na da shekaru 73 a duniya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce mutuwar Shittu wanda dan asalin jihar Kwara ne abin takaici ne.

Sanarwar ta ce:

"Kwamishina Shittu ya kasance mai kokari wurin gudanar da aikinsa inda ya ba da gudunmawa mai tarin yawa ga rundunar 'yan sanda.
"Kafin yin ritaya a watan Agustan shekarar 2011, marigayin ya rike mukamin kwamishinan 'yan sanda a Zamfara da kuma bangaren jin dadin al'umma.

Wasu jihohi Shittu ya yi aiki:

Sanarwar ta kara da cewa:

"Shittu ya shiga aikin dan sanda a shekarar 19 79 inda ya yi aiki a jihohin Zamfara da Kebbi da Ondo da Legas da Imo da Abuja da Edo da Delta da Ebonyi da sauransu."

Kara karanta wannan

Jimami yayin da aka tsinci gawar lakcara a cikin ofishinsa na jami'a, an bayyana halayensa

An haifi Shittu a ranar 23 ga watan Agustan 1950 a Offa da ke jihar Kwara, marigayin ya karatun digiri a Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zari'a inda ya karanta bangaren tarihi.

Tsohon gwamnan Ondo ya rasu

Kun ji cewa, tsohon gwamnan mulkin soja a jihar Ondo, Manjo Janar Ekundayo Opaleye ya riga mu gidan gaskiya a Abeokuta.

Ekundayo ya mulki jihar Ondo da Ekiti a zamanin mulkin Ibrahim Badamasi Babangida tsakanin shekarar 1986 zuwa 1987.

Asali: Legit.ng

Online view pixel