Lokaci Ya Yi: Daga Kwanciya Barci, An Tarar da Gawar Fitaccen Jarumin Fim a Najeriya

Lokaci Ya Yi: Daga Kwanciya Barci, An Tarar da Gawar Fitaccen Jarumin Fim a Najeriya

  • Jarumin masana'antar shirya fina-finai ta Nollywood, Solomon Akiyesi ya riga mu gidan gaskiya bayan fama da gajeruwar rashin lafiya
  • Iyalansa sun bayyana cewa ya kwanta barci bayan ya fara shan maganin gyambon ciki, amma da safe aka tarar da gawarsa a Abuja
  • Shugaban kungiyar AGN, Yakub Abubakar ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga masana’antar fina-finai ta Nollywood

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Fitaccen jarumin masana’antar shirya fina-finai ta Nollywood, Solomon Akiyesi, ya rasu a cikin barcinsa bayan gajeriyar rashin lafiya, lamarin da ya jefa masana’antar cikin jimami.

Shugaban ƙungiyar ‘yan wasan kwaikwayo ta ƙasa (AGN), Yakub Abubakar, ne ya tabbatar da rasuwar a wata sanarwa da ya fitar yau Litinin, 27 ga watan Afrilu, 2026.

Solomon Akiyesi.
Jarumin masana'antar shirya fina-finai ta Nollywood, Solomon Akiyesi Hoto: Solomon Akiyesi
Source: Facebook

Jarumi Solomon Akiyesi ya mutu a Abuja

Kara karanta wannan

Hadimin Tinubu da ya ajiye aiki ya shiga takarar kujerar majalisar tarayya a Kano

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa ‘yar marigayin ta bayyana cewa Akiyesi ya koka da ciwon kirji a daren kafin rasuwarsa, inda aka kai shi asibiti aka gano yana fama da gyambon ciki (ulcer) tare da ba shi magani.

Bayan dawowarsa gida, ya kwanta barci amma bai sake farkawa da safe ba, sai dai aka tarar da gawarsa.

“Matarsa ta yi ƙoƙarin ta tashe shi daga barci da misalin ƙarfe 4:00 na asuba, amma ta yi magana bai amsa ba,” in ji shugaban AGN.

Masana’antar Nollywood ta yi rashi

Yakub Abubakar ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi ga masana’antar fina-finai ta Nollywood, yana mai cewa ƙungiyar na alhini tare da mika sakon ta'aziyya ga iyalansa.

Rahotanni sun nuna cewa an ajiye gawarsa a ɗakin ajiyar gawawwaki a babban birnin tarayya Abuja, inda ya rasu.

Abokan aikinsa sun shiga shafukan sada zumunta suna alhinin rasuwarsa, suna bayyana shi a matsayin jarumi mai ƙwarewa wanda ya taka rawa a fina-finai da zai sa a rika tunawa da shi.

Jaruma Celestina Dovigalle ta bayyana shi a matsayin mutum mai annashuwa, son nishadi da kuzari, tana mai cewa yana kawo farin ciki a duk inda ake daukar fim.

Kara karanta wannan

Yadda minista ya yi murabus duk da Shugaba Tinubu bai so hakan ba

Solomon Akiyesi.
Fitaccen jarumin masana'antar Nollywod ta Kudancin Najeriya, Solomon Akiyesi Hoto: Solomon Akiyesi
Source: Facebook

Takaitaccen bayani kan marigayin

Akiyesi ya yi fice a fina-finai kamar Desperate Ladies, Pretty Liars, Bridge of Contract, Heart of a Saint, Marry Who You Love (2016), Gen Z Wife (2024) da kuma Accidentally Us (2025)

Haka zalika marigayin ya kasance dan asalin garin Ososo da ke ƙaramar hukumar Akoko-Edo ta jihar Edo, ya fara harkar fim tun ƙarshen shekarun 1990

Ya fito a fina-finai sama da 100, inda ya yi suna a matsayin jarumi da kuma mai shirya fina-finai, kamar yadda The Natin ta ruwaito.

Tsohon dan wasan Najeriya ya mutu

A wani labarin, kun ji cewa tsohon dan wasan gaba na Najeriya, Mike Eneramo ya riga mu gidan gaskiya a wurin atisayen motsa jiki a jihar Kaduna.

An ce Eneramo ya gamu da bugun zuciya ne a lokacin da ake tsakiyar atisayen, kuma ya rasu kafin a kai shi asibiti domin samun kulawa.

Eneramo ya yi ritaya daga buga ƙwallon ƙafa a shekarar 2018 bayan ya shafe shekaru yana taka leda a ƙasashen waje, musamman a kasar Turkiyya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262