"Ba Gobe ba ne"; Atiku Ya Yi Muhimmin Kira ga Matasan Najeriya
- Tsohon mataimakin shugaban ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na ADC, Atiku Abubakar, ya ba matasan Najeriya shawarwar
- Atiku ya ce matasa su yi rajista, su tsara kansu tare da shiga harkokin siyasa domin samun damar jagorantar ƙasar
- Ya kuma ce matasa su nemi mukaman siyasa, su riƙa tambayar shugabanni abin da suke yi da amanar da aka damka a hannunsu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Tsohon mataimakin shugaban ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na African Democratic Congress (ADC), Atiku Abubakar, ya yi muhimmin kira ga matasa.
Atiku ya bukaci matasan Najeriya su daina tsaya wa kan yin korafi game da rashin kyakkyawan shugabanci, su shirya karɓar ragamar shugabanci gabanin babban zaɓen 2027.

Source: Facebook
Atiku ya yi wannan kira ne ranar Laraba, 12 ga watan Agustan 2026 yayin da yake jawabi a taron koli na shugabannin matasan ADC na ƙasa da aka gudanar a Abuja, cewar rahoton jaridar Leadership.
Dan takarar shugaban kasar ya bukaci matasan Najeriya su yi rajista, su tsara kansu tare da taka rawar gani a harkokin siyasa, jaridar The Punch ta kawo labarin.
“Kada ku tsaya kawai kuna korafin mutanen da suke yanke shawara. Ku shirya kanku domin maye gurbin waɗanda suke gaza muku,” in ji Atiku.
Atiku ya ce lokacin matasa yanzu ne
Atiku ya ce shekaru da dama ana gaya wa matasan Najeriya cewa su ne shugabannin gobe, yana mai jaddada cewa an yi wa matasa alkawarin “gobe” na tsawon lokaci.
“Lokacinku ba gobe ba ne. Lokacinku yanzu ne,” in ji shi.
Ya ce manufarsa ga matasa ba wai kawai neman goyon bayansu ga burinsa na shugaban ƙasa ba ce, illa ƙarfafa musu gwiwa su mallaki makomar ƙasar.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasan ya soki yadda ake amfani da matasa wajen gangamin yaƙin neman zaɓe, amma a ware su daga yanke shawara bayan kammala zaɓe.
Ya ce matasa sun daɗe suna kasancewa masu amfani ga ’yan siyasa a lokacin yaƙin neman zaɓe, amma bayan zaɓe sai a mayar da su gefe.
A cewarsa, ana tara matasa domin cika wuraren taruka, mamaye kafafen sada zumunta da kare shugabannin siyasa, amma bayan nasara sai su gano cewa har yanzu ana yanke muhimman shawarwari a ɗakunan da ba sa cikin su.
Ya yi alkawarin ba matasa gurbi
Atiku ya yi alkawarin cewa shirin siyasarsa zai samar da gurbi na musamman ga matasa a shugabanci.
Ya ce aƙalla 30% na ’yan takarar majalisa ƙarƙashin jam’iyyar za su kasance ‘yan ƙasa da shekara 40, yayin da adadi mai yawa daga cikinsu zai kasance ‘yan ƙasa da shekara 30.
Sai dai ya bukaci matasan su shirya kansu domin ɗaukar nauyin shugabanci.
“Buɗe ƙofa kaɗai bai isa ba idan waɗanda suka shiga ba su shirya jagoranci ba. Dole ku yi nazarin yadda gwamnati ke aiki, ku fahimci harkokin kuɗaɗen gwamnati da manufofi, ku koyi yadda hukumomi ke aiki, ku fahimci al’ummomin da kuke son wakilta sannan ku shirya kanku domin wahalhalun shugabanci,” in ji shi.

Source: Facebook
Ya bukaci su daina siyasar kafafen sada zumunta
Atiku ya kuma bukaci matasan su wuce matakin fafutuka a kafafen sada zumunta, su zama tsararrun masu shiga harkokin siyasa.
“Fushi ba tsari ba ne. Hashtag ba tsari ba ne. Yin korafi a kafafen sada zumunta ba tsari ba ne."
“Idan kuna son ikon siyasa, dole ku tsara kanku domin samun ikon siyasa. Ku shiga mazabun ku, ku halarci taruka, ku yi tambayoyi, ku nemi a yi wa shugabanni hisabi sannan ku shiga zaɓen waɗanda za su wakilce ku,” in ji shi.
Atiku ya gargadi INEC
A wani labarin kuma, kun ji cewa Atiku Abubakar ya gargadi hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), hukumomin tsaro da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
Atiku Abubakar ya gargade su kan mayar da zaben gwamnan Osun tamkar aikin soja ko amfani da hukumomin gwamnati domin amfanin jam’iyya mai mulki.
Asali: Legit.ng


