Jamhuriyar Nijar Ta Faɗi Ƙasashen da Take Zargi da Yunkurin Yi Mata Juyin Mulki

Jamhuriyar Nijar Ta Faɗi Ƙasashen da Take Zargi da Yunkurin Yi Mata Juyin Mulki

  • Gwamnatin mulkin sojan Nijar ta zargi Faransa da hannu a yunkurin juyin mulkin da aka yi, amma Faransa ta musanta zargin
  • Sojojin da suka yi bore sun kwace wasu wurare a Yamai, ciki har da filin jirgin sama, kafin jami’an tsaro su dakile su
  • Nijar ta ce ta tattara shaidu kan lamarin kuma tana iya kai karar masu hannu a gaban kotunan kasa da kasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Niamey, Niger - Gwamnatin Nijar ta zargi Faransa da hannu a wani yunkurin juyin mulki da aka shirya domin hambarar da gwamnatin mulkin soja.

A baya, Legit Hausa ta ruwaito cewa wasu sojoji sun bar wuraren da suke aikin yaki, sannan suka fara abin da hukumomi suka bayyana a matsayin bore.

Zarge-zarge sun fara yawo kan yunkurin juyin mulki a Faransa
Shugaban mulkin soja a Nijar, Abdourahamane Tchiani da Emmanuel Macron na Faransa. Hoto: Getty Images.
Source: Facebook

Tsakanin ranakun 28 da 29 ga watan Agusta, sojojin sun kwace iko da wasu muhimman wurare, ciki har da filin jirgin saman Diori Hamani da sansanin jiragen sama na 101, cewar Premium Times.

Kara karanta wannan

An rage mugun iri a Arewa, hatsabibin dan bindiga ya bakunci lahira a Zamfara

A sansanin Air Base 101 ne Africa Corps, wata kungiyar sojojin haya ta Rasha, take da sansani.

Har ila yau, sojojin sun yi yunkurin kutsawa cikin yankin fadar shugaban kasa mai tsananin tsaro.

Sai dai bayan shafe sa’o’i ana fafatawa, jami’an tsaro sun fatattaki sojojin da suka yi bore, inda aka kama ko kashe wasu daga cikinsu.

An zargi Faransa

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa gwamnatin Nijar ta sanar a ranar Juma’a, ta gidan talabijin na kasa, cewa bincikenta ya gano cewa wata hanyar sadarwa ce ta taimaka wa bore.

Gwamnatin ta ce Faransa ce ke jagorantar mutanen da ake zargi da hannu wajen shirya harin.

Gwamnatin mulkin sojan ta kuma ce ta tattara “manyan shaidu” kan harin, kuma Nijar na da damar kai lamarin gaban kotunan kasa da kasa.

Faransa ta musanta zargin, inda ta bayyana shi a matsayin “tsantsar kirkira”.

A cewar Sahel Alerte, wata kafar da ke bibiyar yanayin tsaro a yankin, Ministan Harkokin Wajen Faransa, Jean-Noël Barrot, ya ce babu “niyya ko wata hanya” da za ta bai wa Faransa damar kai harin soja kan Nijar.

Kara karanta wannan

An shirya yadda za a yi garkuwa da Mbappe, shugaban Faransa ya yi magana

Zargin ya zo ne kwanaki kadan bayan wani babban kwamandan sojan Nijar ya yi ikirarin cewa kasashe makwabta sun goyi bayan bore.

Roger Gabriel, wani kyaftin na sojan Nijar, ya bayyana a gidan talabijin na gwamnati, inda ya zargi wasu mutane da hannu wajen harin.

Ya ce wasu daga cikin wadanda ke da hannu sun hada da mutanen da ke da alaka da tsohon shugaban kasar, Mohamed Bazoum, da kuma wasu jami’an soji daga Chadi, Benin da Côte d’Ivoire.

Gabriel, wanda shi ne kwamandan Bataliyar Parachute ta 1, wata runduna ta musamman a cikin sojan Nijar, ya ce wasu baki daga Hadaddiyar Daular Larabawa da Belgium sun kira shi.

Ya ce mutanen sun bukace shi da ya shiga cikin bore.

Jami’in ya kuma yi ikirarin cewa sojojin Faransa za su isa Yamai domin taimakawa sojojin da suka yi bore.

A lokacin da aka wallafa rahoton, Benin ya riga ya musanta wannan zargi, yayin da ba a tabbatar da martanin sauran kasashen da aka ambata ba.

Najeriya ta nesanta kanta

Gwamnatin Najeriya ma ta fitar da sanarwa, inda ta nesanta kanta daga yunkurin juyin mulkin da aka yi a Nijar.

Kara karanta wannan

An kama Kirista ta yi shigar Musulunci tana satar yara a Abuja

Karamin Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Sola Enikanolaiy, ya ce akwai “zarge-zargen karya da na mugun nufi” da ke cewa Najeriya da Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka, ECOWAS, sun goyi bayan bore.

Dangantakar Nijar da Faransa ta tabarbare

Dangantakar Nijar da tsohuwar kasar da ta yi mata mulkin mallaka, Faransa, da kuma kawayenta na yankin, ta tabarbare matuka tun bayan da sojoji suka kwace mulki a watan Yulin 2023.

Juyin mulkin ya haifar da rugujewar alakar diflomasiyya tsakanin kasashen, inda gwamnatin mulkin sojan Nijar ta bukaci Faransa ta janye dakarunta.

Daga bisani, Nijar ta kawo karshen doguwar alakar hadin gwiwar soja da Faransa.

Haka kuma, dangantakar Nijar da kawayenta na yankin ta lalace bayan sabbin shugabannin sojan kasar sun yi watsi da tasirin ECOWAS.

Musamman ma, sun ki amincewa da matsin lambar kungiyar na mayar da kasar karkashin mulkin farar hula.

Maimakon haka, gwamnatin mulkin sojan Nijar ta kara karfafa alaka da Rasha, da kuma kasashen makwabta Mali da Burkina Faso, wadanda su ma ke karkashin mulkin soja.

A watan Satumban 2023, kasashen uku suka kafa Kungiyar Kasashen Sahel, AES, wadda aka fara kirkirarta a matsayin yarjejeniyar kare juna.

Kara karanta wannan

Yan bindiga suna lokacinsu a Arewa, sun ƙaƙaba wa Ƴan Sokoto tarar N40m

Daga bisani, an sauya kungiyar zuwa wata kungiyar hadaka ta kasashen Sahel.

A cikin ‘yan shekarun nan, gwamnatin mulkin sojan Nijar ta sha zargin kasashen waje da daukar nauyin haifar da rashin zaman lafiya a kasar.

Sai dai har yanzu ba a samu cikakkun hujjojin da suka tabbatar da wadannan zarge-zarge ba.

Hukumomin Nijar sun magantu kan yunkurin juyin mulki

An ji cewa Jami'an tsaron Nijar tare da taimakon dakarun kasar Rasha sun samu nasarar murkushe yunkurin juyin mulki a Niamey.

Shugaban mulkin sojan kasar, Abdourahamane Tchiani, yana ci gaba da rike madafun iko duk da luguden wuta da aka sha.

Yanayin fargabar da ake ciki na samar da dama ga kungiyoyin 'yan ta'adda na kara bazuwa a cikin Jamhuriyyar Nijar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jarida ne da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.