Trump Ya Fadi 'dalilin' Kai Hari da Wani Matashi Ya Yi a Fadar White House

Trump Ya Fadi 'dalilin' Kai Hari da Wani Matashi Ya Yi a Fadar White House

  • Shugaba Trump ya ce maharin da ya kai hari White House yana da yiwuwar sha’awar fadar tare da yabawa jami’an Secret Service kan gaggawa
  • Nasire Best mai shekara 21 ya bude wuta a kofar tsaro Washington DC jami’an tsaro sun mayar da martani suka kashe shi nan take
  • Bincike ya nuna maharin ya taba karya umarnin kotu ya hana shi kusantar White House sannan ya sha fama da matsalolin bin doka a baya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Washington DC, US - Shugaba Donald Trump ya yi magana bayan wani matashi ya kai hari a fadar White House da ke Amurka.

Trump ya bayyana cewa maharin da ya bude wuta a wajen kofar tsaron Fadar White House na da yiwuwar sha’awar fadar.

Trump ya magantu kan hari a White House
Shugaba Donald Trump na Amurka. Hoto: Anadolu Ajansi.
Source: Getty Images

Rahoton ya tabbatar da cewa Trump ya yabawa jami’an DSS da sauran jami’an tsaro kan gaggawar da suka yi.

Kara karanta wannan

Tinubu ya yi karin haske kan zargin shirin sauya sunan Najeriya, rusa shari'ar Musulunci

Trump ya ce:

“Na gode wa jami’an DSS da sauran jami’an tsaro bisa saurin aiki da kwarewa da suka nuna a daren jiya kan wani maharin da ke kusa da White House, wanda ke da tarihin tashin hankali da kuma yiwuwar sha’awar wannan gini na kasarmu mafi muhimmanci.”

Ya kara da cewa:

“An kashe maharin bayan musayar wuta da jami’an Secret Service a kusa da kofar White House.”

Nasire Best, mai shekara 21, wanda ke dauke da bindiga kirar revolver, ya je kofar tsaro da ke tsakanin titin 17th Street da Pennsylvania Avenue inda ya bude wuta da misalin karfe 6:10 na yamma.

Best ya harba harsasai da dama kafin jami’an tsaro masu saurin daukar mataki su hallaka shi a daya daga cikin wuraren tsaro da ke kewaye da fadar White House.

Rahotanni sun bayyana cewa Best, wanda ya yi imani shi Annabi Isa ne, an san shi sosai ta Secret Service saboda yawan yawo a wuraren shiga fadar, kuma ya saba karya umarnin kotu da ke hana shi kusantar White House.

Kara karanta wannan

Iran da Amurka: An samu sauyin farashin mai a duniya yayin da ake tattaunawar sulhu

An kama shi a baya a watan Yuli 2025 lokacin da ya yi kokarin ketare shingen tsaro ba tare da izini ba, inda ya ki bin umarnin jami’an tsaro yana ikirarin shi Annabi Isa kuma yana rokon a kama shi, kamar yadda Associated Press ta ruwaito.

An kuma fitar da umarnin kotu na hana shi kusantar fadar White House, sannan daga baya aka sake fitar da sammacin kotu saboda rashin halarta a shari’a.

Jami’an Secret Service sun gaggauta kulle fadar White House tare da umartar ‘yan jarida su taru a yankin north lawn sannan su shiga dakin taron manema labarai. Bayan kusan mintuna 30, an dage dokar kullewa.

Jami’an tsaro na Secret Service da sauran jami’an ‘yan sanda sun kasance a wajen fadar bayan harbe-harben da aka ji a ranar 23 ga Mayu, 2026.

Trump ya yi amfani da wannan hari a matsayin dalili na kara karfafa gina sabon dakin taro (ballroom) na Fadar White House wanda zai maye gurbin bangaren Gabas.

Ya ce wannan lamari ya nuna muhimmancin samar da mafi tsaro ga dukkan shugabanni na gaba, inda ya kara da cewa tsaron kasa na bukatar hakan.

Trump da uwargidansa Melania Trump sun halarci taron White House Correspondents’ Dinner a Washington Hilton a ranar 25 ga Afrilu, inda wani da ake zargi, Cole Allen, ya bude wuta a wajen dakin taron, ya ji wa jami’in DSS rauni.

Kara karanta wannan

Juyin mulki: Ma'aikacin Aso Villa ya tona yadda aka shirya kutsa wa fadar shugaban kasa

Trump ya kasance a White House a ranar Asabar, inda ya bayyana cewa ya kammala kiran waya mai muhimmanci da shugabannin kasashen Gabas ta Tsakiya kan kokarin cimma yarjejeniyar zaman lafiya da Iran.

Karin bayani na tafe....

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.