Matashin Sojan Israila Ya Bakunci Lahira bayan Harin Mayakan Hezbollah
- Mayakan kungiyar Hezbollah sun harba makamai kan rukunin sojojin Isra'ila da ke a Kudancin kasar Lebanon
- Daya daga cikin makamin ya fashe a kusa da wani sojan Isra'ila, wanda ya bar duniya duk da kokarin ceto shi da aka yi
- Rundunar sojojin Isra'ila ta bayyana cewa sojan ya mutu ne yayin fafatawa a Kudancin Lebanon inda ake ci gaba da musayar hare-hare duk da yarjejeniyar tsagaita wuta
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Birnin Tel-Aviv, Isra'ila - Rundunar sojojin Isra’ila (IDF) ta sanar da cewa mayakan Hezbollah sun hallaka daya daga cikin sojojinta Lebanon.
Rundunar IDF ta bayyana cewa Staff-Sgt. Negev Dagan, ɗan shekara 20 daga Dekel, ya mutu lokacin fafatawa a Kudancin Lebanon.

Source: Getty Images
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da rundunar IDF ta sanya a shafinta na X a ranar Juma'a 15 ga watan Mayun 2026.
Sojan Isra'ila ya mutu a Lebanon
Negev Dagan ya ji rauni ne lokacin da mayakan Hezbollah suka harba makamin igwa zuwa rukunin sojojinsa da ke gudanar da aiki kusa da Kogin Litani. Ɗaya daga cikin harsashin makamin ya fashe kusa da Dagan.
Likitocin fagen fama sun yi ƙoƙarin ba shi taimakon gaggawa a wurin, amma tilas ta sanya suka tabbatar da mutuwarsa.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10:00 na dare. Negev Dagan ya yi aiki ne a Bataliya ta 12 ta Brigade na Golani.
An ƙara masa girma bayan mutuwarsa daga Sergeant zuwa Staff-Sergeant. Dagan shi ne soja na shida da ya faɗi a fagen fama tun bayan da yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta ta fara aiki.
Hezbollah ta kai hari kan sojojin Isra'ila
Tashar Aljazeera ta ce tun da farko Hezbollah ta ce ta "kai hari kan taron sojojin makiya na Isra’ila a rukunin Rosh Hanikra [Ras an-Naqoura]" kusa da iyakar Lebanon da jirgi mara matuƙi.
Dakarun sojojin Isra’ila sun bayyana cewa "farar hula na Isra’ila da dama sun ji rauni kuma an kwashe su domin ba su kulawar likita" bayan wani jirgi mara matuƙi da ƙungiyar ta harba.

Source: Twitter
Ana tattaunawa tsakanin Isra'ila, Lebanon
Hakan na zuwa ne yayin da aka fara zagaye na uku na tattaunawa kai-tsaye tsakanin Isra’ila da Lebanon a Washington, DC, kwanaki kaɗan kafin karewar "yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta" wadda kusan ba ta dakatar da hare-haren Isra’ila da martanin Hezbollah gare su ba.
Tattaunawar, wadda aka fara ranar Alhamis, 14 ga watan Mayun 2026, ta samu halartar manyan wakilai daga Lebanon da Isra’ila bayan zaman share fage na farko da jakadun ƙasashen biyu a Washington suka jagoranta.
Isra'ila ta hukunta sojojinta
A wani labarin kuma, kun ji cewa rundunar sojojin Isra'ila (IDF) ta hukunta wasu sojojinta da suka ci mutuncin mutum mutumin mamar Yesu Almasihu.
Rundunar IDF ta ta bayyana cewa ta yanke wa wasu sojoji biyu hukuncin ɗauri a gidan kurkuku bayan kammala bincike kan zargin da ake yi masu.
Ta bayyana cewa yanke hukuncin ne bayan an ɗauki ɗaya daga cikinsu hoto yana sanya tabar sigari a bakin mutum-mutumin mamar Yesu Almasihu a Kudancin Lebanon.
Asali: Legit.ng

