Ba Tsoro: Gargadin da Tawagar Iran Ta Yi Wa Amurka yayin Tattaunawa a Pakistan

Ba Tsoro: Gargadin da Tawagar Iran Ta Yi Wa Amurka yayin Tattaunawa a Pakistan

Shugaban majalisar dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya tuna baya kan abin da ya faru yayin tattaunawa da Iran

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ghalibaf ya bayyana cewa shi da kansa ya gargadi tawagar Amurka gaba da gaba kan mashigar ruwa ta Hormuz

Shugaban majalisar dokokin ya bayyana cewa gargadin ya tilastawa tawagar Amurka sanyawa jirgin ruwan kasar ya koma baya

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Birnin Tehran, Iran - Shugaban majalisar dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya bayyana wani abu da ya faru yayin tattaunawa da Amurka.

Mohammad Bagher Ghalibaf ya bayyana cewa shi da kansa ya gargaɗi tawagar Amurka a Islamabad game da ta’azzara rikici a mashigar ruwa ta Hormuz.

Tawagar Iran ta ja kunnen Amurka
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump da shugaban majalisar dokokin Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Tashar Press tv ta ce Ghalibaf ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka fitar a ranar Asabar, 18 ga watan Afirilun 2026.

Kara karanta wannan

A karon farko bayan bude Hormuz, an hango jirgin mai na wuce wa ta Iran

Wane gargadi Iran ta yi wa Amurka?

Ghalibaf ya ce ya gargaɗi tawagar Amurkar da ta zo babban birnin Pakistan don tattaunawar tsagaita wuta cewa dakarun Iran za su buɗe wuta kan jiragen kwashe nakiyoyi idan har suka matsa ko da "inci ɗaya" daga inda suke a wannan muhimmiyar hanyar ruwa.

Babban ɗan majalisar dokokin na Iran kuma jagoran tattaunawa ya bayar da cikakken bayani kan taho-mu-gama da aka yi tsakanin dakarun sojan ruwan Iran da sojojin Amurka a mashigar Hormuz.

Ghalibaf ya jaddada cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da cikakken iko a kan mashigar Hormuz kuma tuni ta tilastawa Amurka ja da baya.

"Na gayawa tawagar Amurka cewa idan jirginsu na kwashe nakiyoyi ya motsa ko da kaɗan daga inda yaje tabbas za mu bude masa wuta."

- Mohammad Bagher Ghalibaf

Jirgin Amurka ya juya baya

Shugaban majalisar dokokin ya ƙara da cewa tawagar Amurkar ta nemi tsawon mintuna 15 domin isar da umarnin cewa jirgin ya juya baya.

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Iran ta sake kunyata Trump a idon duniya ana shirin sake zaman sulhu

Ghalibaf ya ƙara da cewa rundunar sojan ruwa ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) ta dakile wani yunƙuri na gudanar da aikin kwashe nakiyoyi, wanda ya ce ya saɓawa yarjejeniyar tsagaita wuta.

"Mun ci gaba har zuwa ga gabar da za a yi arangama, amma sai makiyi ya ja da baya."

- Mohammad Bagher Ghalibaf

Iran za ta ci gaba da iko da mashigar Hormuz

Kakakin majalisar dokokin ta Iran, wanda ya jagoranci tawagar Iran don tattaunawa da tawagar Amurka a Islamabad a makon da ya gabata, ya ce mashigar Hormuz tana ƙarƙashin ikon Jamhuriyar Musulunci ne.

Ya kuma yi watsi da matakin baya-bayan nan na gwamnatin Trump na "killace tashoshin ruwan Iran" a mashigar Hormuz, inda ya kira shi a matsayin "shawara ta sakaci da aka ɗauka cikin jahilci."

Ghalibaf ya gargadi tawagar Amurka
Mohammad Bagher Ghalibaf tare da tawagar Iran bayan sun isa Pakistan Hoto: @Visegrad
Source: Twitter
"Ba zai yiwu wasu su riƙa wucewa ta mashigar Hormuz ba amma mu a hana mu. Idan Amurka ba ta janye killacen ba, lallai zirga-zirga a mashigar Hormuz za ta fuskanci takunkumi."
"Idan har ana yin wata zirga-zirga a mashigar a yau, to ikon mashigar yana hannunmu ne."

- Mohammad Bagher Ghalibaf

Kara karanta wannan

Abin mamaki: Amurka ta taimaki kasar Musulunci ta Iran, ta yi abin alheri a Hormuz

Jagoran Iran ya aika da sako

A wani labarin kuma, kun ji cewa sabon jagoran addini na kasar Iran, Mojtaba Khamenei, ya yabawa dakarun sojojin kasar.

Mojtaba Khamenei ya jinjinawa dakarun ne saboda jarumtakar da suka nuna wajen kare ƙasar a yaƙin da aka tilastawa kasar.

Jagoran ya kuma karrama daukacin kwamandojin da suka jagoranci rundunar sojojin Iran a cikin shekaru 50 da suka gabata.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com