Rikicin PDP
Hadakar Atiku ta ce sauya shekar gwamnonin PDP ba abin mamaki ba ne, tana zargin wasu da yin aiki da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu kafin 2027.
Usman Bugaje ya ce jam'iyyar APC na amfani da kuɗi da barazana wajen janyo ‘yan adawa, yana mai cewa hakan na rushe siyasa da dimokuraɗiyyar Najeriya.
Gwamnan jihar Delta, Sheriff Obovrevwori, ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC a ranar Laraba, sakamakon rikici da ya mamaye PDP da wasu matsalolin siyasa a jihar.
Magoya bayan Wike a PDP sun kafa sababbin shugabanni a Edo da Bayelsa, inda ake zargin rikicin fidda gwani da gangamin Bayelsa ne suka jawo wannan barakar.
Yarjejeniyar sirri da ake zargin an kulla tsakanin Tinubu da gwamnoni na PDP na ƙara rura rikicin shugabanci a jam'iyyar, yayin da Tinubu ke neman tazarce a 2027.
Tsohon gwamnan Delta kuma mataimakin Atiku Abubakar a takarar zaben 2023, Ifeanyi Okowa da wasu jiga-jigan PDP sun koma jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya.
Gwamnatin Akwa Ibom ta musanta rade-radin cewa Gwamna Umo Eno na shirin ficewa daga PDP zuwa APC a kasa bayan takwaransa na Delta, Sheriff Oborevwori ya gudu.
Wani ɗan majalisar wakilan tarayya, Oluwole Oke, ya fice daga jam'iyyar PDP. Sai dai bai bayyana jam’iyyar da zai koma ba, amma ya nemi mabiyansa da su bar PDP.
Tsohon mataimakin shugaban PDP, Cif Bode George ya nuna takaici kan yunƙurin sauya shekar gwamnoni 4 zuwa APC, ya ce wannan abin kunya ne a siyasa.
Rikicin PDP
Samu kari