Jihar Kaduna
Uwar gida, Zaliha Shuaibu ta amsa laifin kashe jaririn kishiyarta a Kaduna, ta ce Lawal Muhammad, ƙanin mijinta, ne ya ba ta gubar da ta kashe yaron da ita.
Shugaban hadaddiyar kungiyar masu shirya fim a Kannywood, Umar Maikudi da aka fi sani da Cashman ya rasu a Zariya. Ali Nuhu da Abba El-Mustapha sun yi ta'aziyya.
Rahotanni sun tabbatar da cewa kotun Majistare a Kaduna ta gurfanar da Abigail Victor mai shekara 23 bisa zargin caka wa saurayinta wuka saboda zargin yaudara.
A kokarin inganta harkokin shugabanci, Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya yi nadin sababbin kwamishinoni domin kawo sauye-sauye da jagoranci na gari.
Sheikh Musa Assadus Sunnah ya yi magana a bidiyo inda ya ƙaryata rahoton kama yan uwan Ado Aliero a Saudiyya inda ya ce babu wata hujja da ke nuna suna da alaƙa.
Wasu yan APC a Kaduna sun nemi Shugaba Tinubu da Gwamna Uba Sani da su fara shirin tsayawa takara a 2027, domin za su samu goyon bayansu a rumfunan zabe.
Gwamnan Kaduna Malam Uba Sani ya bayyana cewa ba za su iya warware matsalar tsaro nan da shekara 10 ba, amma ya ce lokaci ya yi da ƴan Arewa za su haɗa kai.
Sheikh Ishaq Adam Ishaq ya yi tsokaci kan halartar shirin Gabon 'Talkshow' da Alkali Abubakar Salihu Zaria ya yi inda ya ce ba laifi ba ne a addinance.
Sheikh Alƙali Abubakar Salihu Zariya ya bayyana a shirin Hadiza Gabon wanda ya haifar da muhawara a kafafen sada zumunta, inda ra’ayoyi suka bambanta matuƙa.
Jihar Kaduna
Samu kari