Wahalar man fetur a Najeriya
Kamfanin man fetur na kasa (NNPC) ya sanar da fara hako man fetur a wata sabuwar rijiya a jihar Akwa Ibom. Kamfanin ya bada sanarwar ne a jiya Lahadi.
Gwamnatin jihar Anambra ta sha alwashin rufe gidajen mai da ke kara farashi da kuma cakuda mai da wasu abubuwa hade da sauya yanayin lita domin samun riba.
Hukumar hana fasa kwauri ta ce ta damke lita 12,435 na man fetur wanda kudinsa ya kai Naira miliyan 10.8 a hanyar Cameroon. An kuma kama jarka 61 a hanyar Benin.
Shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Opeyemi Bamidele, ya bai wa yan Najeriya tabbacin kawo karshen wahalar man fetur da suke fuskanta ba da jimawa ba.
Hukumar IMF ta nuna damuwa kan yadda Shugaba Bola Tinubu ya dawo da tallafin mai a boye inda ta ce hakan asara kawai zai jawowa Najeriya na biliyoyi.
Hukumar kare afkuwar hadurra ta kasa (FRSC) ta gargadi masu ababen hawa kan daukar fetur a cikin jarkoki idan suna tafiya. Hukumar ta ce hakan zai haddasa gobara.
Gwamnatin Tarayya ta shirya sake binciken ikirarin kamfanin mai na NNPCL game da bashin N2.8trn na tallafi da ya ke bin gwamnatin tun kafin cire tallafin mai.
Gwamnatin tarayya ta ce za ta sayar da rijiyoyin mai 17 a yayin sabunta lasisin rijiyoyin na 2024. SGwamnatin ta ce 'yan kasuwa ne kadai zata sayarwa rijiyoyin.
Kamfanin man fetur na Najeriya (NNPC) ya ce ya tanadi mai lita biliyan 1.5 domin wadatar da al'ummar Najeriya. Jami'in yada labaran kamfanin ne ya bada sanarwar.
Wahalar man fetur a Najeriya
Samu kari