Gobara
Wata mata ta garkame yaranta kanana biyu a cikin daki inda ta shiga makwabta. Sai dai cike da rashin sa’a gobara ta kama tare da lashe rayukan yaran biyu duka.
Hukumar kashe gobara ta jihar Legas da Ogun sun tabbatar da tashin wata gobarar cikin dare a fitacciyar kasuwar Ajimula dake tsakanin iyakokin Ogun da Legas.
Mummunar Gobara a jihar Jigawa ta lashe rayukan wata matar aure da ‘ya’yanta biyu yayin da suke bacci a bukka. Ana zaton rushin da suka kai ne ya tada gobarar.
Wata gobara wacce har a halin yanzu ba a san abinda ya tada ta ba ta lamushe wata ma’ajiyar kayayyaki a wani bene mai hawa uku dake Legas wacce ta tada hankula.
Yanzu muke samun labarin yadda wata mummunar gobara ta kama a hedkwatar tsaro ta Najeriya. An yi nasarar shawo kan wutar kamar yadda hukumar tsaron ta tabbatar.
Wata mummunan gobara da ta shafi tankokin man dizal guda 5 a Kano ta janyo asarar dizal kimanin lita 20,400 a cewar mai magana da yawun hukumar SFS na Kano
Wani bawan Allah mai suna Choephel Norbu ya banka wa gidan cin abinci wuta saboda ya fushin da ya yi bayan an kawo masa wani abin daban da wanda ya bukata.
Gagarumar gobara ta tashi a babbar kasuwar garin Kachako dake karamar hukumar Takai ta jihar Kano inda ta lakume shaguna 150 na ‘yan kasuwa.An ceci shaguna 800.
Mummunar gobara ta tashi a tsangaya Model Boarding school dake kauyen Kiyawa na karamar hukumar Bagwai ta jihar Kano. ta cinye aji 14, ofisoshi 12 da sauransu.
Gobara
Samu kari