Yaki da ta'addanci a Najeriya
Jami'an tsaro na Operation Hadarin Daji da ke Arewa maso Yamma sun yi nasarar cafke wani ciyaman din jam'iyya na gunduma a Zamfara da ake zargi da safarar bindigu.
Tsagerun ƴan bindiga sun yi awon gaba da shugaban hukumar kula da tashohin manyan motoci na jihar Oyo, Alhaji Akeem Akintola, maharan sun shiga har gidansa.
Gwarazan dakarun sojojin Najeriya sun yi nasarar murkushe ƴan bindiga uku a wani Operation da suka yi a kauyen Chibi, jihar Taraba, aun kwato muggan makamai.
Rundunar ƴan sanda ta musamman da IGP ya kafa da kuma dakarun hukumar ƴan sandan Abuja sun sheƙe wani ɗan bindiga da aka jima ana nema ruwa a jallo a Bwari.
Miyagun yan bindiga sun kai hari yankin ƙaramar hukumar Batsari a jihar Katsina, sun yi ajalin mutum biyu tare da yin awon gaba da wasu 29 ranar Talata da ta wuce.
Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana cewa wani makiyayi da ya kashe ɗan garin mangu, da yunkurin satar shanu na cikin abubuwan da suka kawo tashin hankali a Filato.
Rundunar ƴan sandan jihar Filato ta nuna mutum 17 da aka kama da zargin hannu a hare-haren da aka kananan hukomomin Bokkos, Barkin Ladi da Mangu.
A koƙarin kwato wuraren da ke hannun ƴan ta'adda a jihar Borno, sojoji da sauran jami'an tsaro sun faɗa tarkon mayakan Boko Haram, an rasa rayukan jami'an tsaro 3.
Dakarun sojoji sun samu nasarar ragargazar yan ta'adda a jihar Kebbi. Dakarun sojojin sun kuma ceto mutanen da yan ta'addan suka yi garkuwa da su.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari