Peter Obi Ya Kinkimo Batun da Yan Najeriya Suka Dade Suna Son Sani game da Tinubu

Peter Obi Ya Kinkimo Batun da Yan Najeriya Suka Dade Suna Son Sani game da Tinubu

  • Peter Obi ya bukaci Shugaba Bola Tinubu ya yi wa ’yan Najeriya cikakken bayani kan wasu batutuwan da suka shafi tarihinsa, musamman karatunsa
  • Obi ya ce ya kamata ’yan Najeriya su samu bayani bayyananne, sahihi kuma mai iya tabbatarwa kan karatun shugaban
  • Tsohon gwamnan Anambra ya ce ofishin shugaban kasa ya kamata ya zama abin koyi wajen gaskiya, rikon amana da bayyana gaskiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Dan takarar shugaban kasa na NDC, Peter Obi, ya bukaci Shugaba Bola Tinubu ya yi wa ’yan Najeriya cikakken bayani kan batutuwan da suka shafi tarihinsa, ciki har da tarihin karatunsa.

Obi ya ce ’yan Najeriya sun cancanci samun amsoshi kan batutuwan da suka shafi al’umma, musamman a daidai lokacin da ake samun rahotannin cewa shugaban kasar na kokarin hana bayyana wasu bayanan tarihinsa a wata kotun kasar waje.

Kara karanta wannan

'Na san ainihin shekarun shugaba Tinubu': Atiku ya ce yana da hujjoji masu ƙarfi

Peter obi.
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar NDC, Peter Obi Hoto: Peter Obi
Source: Facebook

Tsohon gwamnan jihar Anambra ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Litinin, 31 ga Agusta, 2026.

Ya bayyana matakin shari’ar da aka ruwaito cewa abin kunya ne, yana mai cewa bai kamata shugaban kasa mai ci ya nemi hana binciken sahihan bayanai da suka shafi tarihinsa ba.

Peter Obi ya nemi karin bayani

Obi ya ce abin takaici ne ganin yadda aka kai ga wani matsayi da shugaban kasa mai ci ke neman wata kotun kasar waje ta hana bayyana bayanan da suka shafi tarihinsa, musamman wadanda suka shafi al’amuran jama’a.

Ya ce ya kamata a yi wa ’yan Najeriya bayani kan dalilin da ya sa batutuwan da suka shafi karatun farko na shugaban kasa, musamman makarantun firamare da sakandare, suka ci gaba da zama ba a warware su ba.

A cewarsa, bai kamata a dogara da shari’a kawai wajen magance tambayoyin da jama’a ke yi kan irin wadannan bayanai ba.

Kara karanta wannan

Ana wata ga wata: Atiku ya gano shaidar da ke nuna asalin shekarun Bola Tinubu a duniya

Obi ya ce ’yan Najeriya sun cancanci samun “bayani bayyananne, sahihi kuma wanda zai gamsar da su” kan batutuwan, musamman idan an taba gabatar da bayanan karatun a baya.

Obi ya kalubalanci fadar shugaban kasa

Dan takarar NDC ya jaddada cewa fadar shugaban kasa ya kamata ta kasance abin koyi wajen rikon amana, gaskiya, bayyana gaskiya da shugabanci mai bin ka’ida.

Obi ya ce Najeriya ta fi karfin mutum guda, don haka ya kamata a fifita martabar kasa da mutuncinta a kan muradun kowane mutum.

Bola Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu yana jawabi a wata ziyara da ya kai domin kaddamar da ayyuka a Katsina Hoto: Ibrahim Kaula Mohammed
Source: Facebook

Ya kara da cewa batutuwan da suka shafi mutuncin ofishin shugaban kasa ya kamata a yi musu bayani cikin gaskiya da sahihanci domin amfanin ’yan Najeriya.

Obi ya jaddada cewa duk wani batu da ya shafi mutuncin ofishin shugaban kasa ya kamata a yi bayani cikin gaskiya da sahihanci, domin kare amana da martabar Najeriya.

Peter Obi ya goyi bayan cire tallafi

Kun ji cewa Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar adawa ta NDC, ya sake jaddada goyon bayansa ga cire tallafin man fetur a Najeriya.

Ya ce abin da ya kamata gwamnati ta yi shi ne ta samar wa ’yan ƙasa wasu hanyoyin amfani da kuɗin da aka tara bayan cire tallafin, domin inganta walwala da jin dadinsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262