Magana Ta Fito: An Ji Dalilin da Ya Sa Malaman Musulunci Suka Goyi Bayan Tinubu a 2027
- Sama da malaman Musulunci 500 daga jihohin Arewa 19 da Abuja ne suka bayyana goyon bayansu ga sake zaben Bola Tinubu a 2027
- Ministan Gidaje, Muttaka Rabe Darma ya fito ya yi karin haske kan dalilin malaman na daukar wannan mataki
- Taron malaman ya yaba da inganta tsaro a Kaduna, Katsina da Sokoto, tare da neman ƙarin aiki a Neja da Zamfara
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abuja, Nigeria - Ministan Gidaje da Raya Birane, Muttaka Darma Rabe, ya fito ya yi bayani kan goyon bayan malaman Musulunci ga tazarcen Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027.
Tun farko dai an bayyana cewa malaman Musulunci 500 daga jihohin Arewa 19 da Abuja sun amince da sake zaben Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin ya yi shekara takwas a kan mulki.

Source: Facebook
Tribune Nigeria ta ce malaman sun bayyana hakan ne a ƙarshen wani taron dabarun siyasa da aka gudanar a Dutse, babban birnin Jihar Jigawa, ranar Asabar, inda aka tattauna kan abubuwan da gwamnatin Tinubu ta cimma a Arewa.
Taron ya samu halartar gwamnoni shida na Arewa, ciki har da Uba Sani na Kaduna, Dikko Radda na Katsina, Mala Buni na Yobe da Umar Namadi na Jigawa.
Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin, da mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin siyasa, Kabir Ibrahim Masari, da wasu manyan jami’an gwamnati sun halarci taron.
Malamai sun goyi bayan Tinubu
Da yake karanta ƙudurin taron, Rabe Darma ya ce an gayyaci malaman Musulunci, masu wa’azi da masana daga jihohin Arewa 19 da Abuja domin tattauna ci gaban da yankin ya samu tun bayan hawar gwamnatin Tinubu.
“Fiye da malaman Musulunci, masu wa’azi da limamai 500 daga jihohin Arewa 19 da Abuja sun kada ƙuri’ar amincewa da Shugaba Bola Tinubu tare da yin kira da a goyi bayan sake zabensa a 2027.”
Ministan ya ce taron malaman Musulunci ya yi nazari kan ayyukan gwamnatin Tinubu, inda ya gano cewa gwamnati na samun ci gaba a fannonin tsaro, ababen more rayuwa da raya Arewa.

Source: Twitter
Dalilin malamai na goyon bayan Tinubu
A cewar Rabe, taron ya nuna cewa an samu sauƙin matsalolin tsaro a Kaduna, Katsina da Sokoto, duk da cewa har yanzu akwai buƙatar ƙarin aiki a jihohin Niger da Zamfara.
Taron ya kuma mayar da hankali kan gyaran babbar hanyar Kano zuwa Kaduna, inda malaman suka bayyana ta a matsayin muhimmiyar hanya ga harkokin kasuwanci da tattalin arzikin yankin.
Ya ce malaman sun duba ci gaba da aka samu, bisa haka suka ga ya dace su karwa Tinubu baya a karo ma biyu.
Tinubu zai iya kayar da Kwankwaso a Kano
Kun ji cewa Hon. Abdulmumin Jibrin ya ce Shugaba Bola Tinubu zai kayar da Rabiu Kwankwaso a Kano a zaben shugaban kasa na 2027.
Dan majalisar, wanda a baya ya kasance abokin siyasar Kwankwaso amma yanzu yake APC mai mulki, ya ce sanin tsarin siyasar Kwankwaso zai taimaka musu wajenNsamun galaba a kansa.
Jibrin ya amince Kwankwaso na da karfin fada aji a Kano, amma ya ce kasancewarsa dan takarar mataimakin shugaban kasa zai sauya lamarin
Asali: Legit.ng

