Wata Sabuwa: Gwamnoni 18 da ke Neman Tazarce a Zaben 2027 Sun Sa Labule a Kebbi

Wata Sabuwa: Gwamnoni 18 da ke Neman Tazarce a Zaben 2027 Sun Sa Labule a Kebbi

  • Gwamnonin jam'iyyar APC 18 da ke wa'adin farko a kan mulki sun shiga wata ganawar sirri a gidan gwammatin jihar Kebbi
  • Gwamna Nasir Idris na Kebbi ne ya karɓi baƙuncin taron wanda rahotanni suka nuna yana ci gaba da gudana yanzu haka a Birnin Kebbi
  • Bayanai sun nuna cewa gwamnonin APC biyu ba su samu halartar taron amma amma sun aika da sakon neman uzuri da kuma bada hakuri

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Birnin Kebbi, Nigeria - Gwamnoni 18 na jam'iyyar APC da ke wa'adin farko a kan karagar mulki sun shiga wani taron gaggawa a Birnin Kebbi, babban birnin jihar Kebbi.

Rahotanni sun nuna cewa gwamnonin, wadanda ke shirin neman wa'adi na biyu a zaben 2027 da ke tafe, sun shiga taron ne a fadar gwamnatin Kebbi yau Talata, 7 g watan Yuli, 226.

Kara karanta wannan

Gwamna Alia ya bugi kirji, ya fadawa Tinubu yawan kuri'un da zai samu a Benue

Gwamna Nasir Idris.
Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idrishana jawabi a taron majalisar zartarwa a Birnin Kebbi Hoto: Dr. Nasir Idris Kauran Gwandu
Source: Facebook

Gwamna Nasir ya karɓi baƙuncin taron

Jaridar Leadership ta ruwaito cewa gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris wanda yana daya daga cikin gwamnonin da ke wa'adin farko, shi ne ya karɓi baƙuncin taron.

Taron ya samu halartar galibin gwamnonin APC da ke wa’adin farko daga jihohi daban-daban na ƙasar domin tattauna muhimman batutuwan da suka shafi jam’iyyar da kuma harkokin mulkin ƙasa.

Har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto, taron na ci gaba da gudana a cikin sirri yayin da ‘yan jarida ke jiran sanarwar abin da aka cimma nan ba da jimawa ba.

Jihohin da suka halarci taron

Daga cikin gwamnonin da suka halarci taron akwai na jihohin Sokoto, Kaduna, Jigawa, Plateau, Delta, Ekiti, Taraba, Ondo, Ebonyi, Akwa Ibom, Edo, Benue, Kogi da Enugu, tare da sauran jihohin da APC ke mulki.

Sai dai gwamnonin jihohin Cross River, Niger da Katsina ba su samu halartar taron ba, bayan sun aika da saƙon neman afuwa kan rashin halartarsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262