Bayanai Sun Fito: An ji dalilin Tinubu da APC na Kin Marawa Fubara Baya domin Takara

Bayanai Sun Fito: An ji dalilin Tinubu da APC na Kin Marawa Fubara Baya domin Takara

  • Gwamna Siminalayi Fubara ya rasa goyon bayan Shugaba Bola Tinubu da jam'iyyar APC a Rivers
  • Majiyoyin APC sun ce an hana Fubara tikitin takarar gwamna a 2027 saboda yarjejeniyar da ya amince ba zai nemi wa’adi na biyu ba
  • Kungiyoyin matasan Kudu maso Kudu da magoya bayan Fubara sun nuna takaici kan janyewarsa daga takara

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Port Harcourt - Sababbin bayanai sun bayyana yadda gwamnan Rivers, Siminalayi Fubara kan dalilin janyewa daga takara.

Majiyoyi sun Fubara ya rasa goyon bayan Shugaba Bola Tinubu da shugabannin APC a rikicin siyasa tsakaninsa da Nyesom Wike.

An gano dalilin Tinubu da APC na kin marawa Fubara baya
Gwamna Siminalayi Fubara, Nyesom Wike da Bola Tinubu. Hoto: Nyesom Wike, Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Twitter

Rahotanni daga Punch sun nuna cewa Fubara ya sabawa yarjejeniyar sulhu da aka cimma tsakaninsu bayan rikicin siyasar jihar ya yi kamari.

Wani mamba na kwamitin gudanarwar APC ya bayyana cewa shugabancin jam’iyyar bai yi wa Fubara tarba ta musamman bayan sauyawa APC ba saboda bai samu amincewar Wike ba.

Kara karanta wannan

'Mutumina ne': Peter Obi ya yi magana da ake zargin yana gujewa Atiku

Ya ce Tinubu ya mika tsarin siyasar Rivers ga Wike, sannan ya shawarci Fubara ya mayar da hankali kan mulki.

Majiyar ta kara da cewa shugaban kasa ya taba ceton Fubara daga yunkurin tsige shi sau biyu, amma daga baya an cimma yarjejeniya cewa ba zai nemi wa’adi na biyu ba.

Ta ce Wike yana yawan fadin “yarjejeniya yarjejeniya ce” saboda Fubara ya taba amincewa da hakan.

Rahotanni sun ce wasu jiga-jigan APC sun yaudari Fubara da alkawarin goyon bayan jam’iyya, alhali shugaban kasa da kungiyar gwamnoni ba sa tare da shi.

Haka kuma an ce an hana duk ‘yan takararsa shiga zaben fidda gwani na majalisar dokoki da ta tarayya.

Wata majiya daga APC a Abuja ta ce kwamitin tantance ‘yan takarar gwamna karkashin jagorancin shugaban jam’iyya, Farfesa Nentawe Yilwatda, bai tantance Fubara ba.

Ta ce ya fusata tare da fita daga wajen tantancewar bayan an sanar da shi cewa ba zai tsaya takara karkashin APC ba.

Wani kusa da Wike ya tabbatar da cewa APC ta hana Fubara tsayawa takara domin mutunta yarjejeniyar da aka cimma tun bayan rikicin siyasar jihar.

Kara karanta wannan

Takarar 2027: Yadda Abba Kabir Yusuf ya sasanta manyan 'yan APC a Kano

Ya ce Fubara ya tsira daga tsigewa ne saboda taimakon Tinubu da Wike, saboda haka dole ya cika alkawarin da ya dauka.

Jam’iyyar APC ta ki shirya wa Fubara tarbar shiga jam’iyya duk da cewa ya koma APC a watan Disambar 2025. Sauran gwamnoni daga PDP kamar Sheriff Oborevwori da Umo Eno sun samu tarba ta musamman daga shugabannin APC, amma Fubara bai samu irin wannan kulawa ba.

Shugaban APC, Yilwatda, ya bayyana cewa rashin yi wa Fubara tarba ya samo asali ne daga dabarun siyasa da kuma kula da yanayin watan Ramadan a Arewa.

Ya ce jam’iyyar ta fara karbar gwamnoni daga Arewa kafin ta karkata zuwa Kudancin Najeriya.

Bincike ya nuna cewa Fubara ya tsallake yunkurin tsige shi har sau uku tun bayan hawansa mulki. Yunkurin farko ya faru ne a watan Oktoban 2023 lokacin da ‘yan majalisa 24 suka rattaba hannu kan bukatar tsige shi.

Bayan rikicin ya kara kamari a watan Maris na 2025, Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-baci a Rivers tare da dakatar da Fubara da mataimakiyarsa Ngozi Odu da ‘yan majalisar jihar na tsawon watanni shida.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.