Ana Shirin Zaben 2027, Malamin Duba Ya Gargadi Atiku kan Sake Tsayawa Takara

Ana Shirin Zaben 2027, Malamin Duba Ya Gargadi Atiku kan Sake Tsayawa Takara

  • Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya samu gargadi kan sake tsayawa takara a 2027 da ake tunkara a Najeriya
  • Malamin duba, Satguru Maharaj Ji wanda ya gargadi Atiku ka da ya tsaya takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2027 mai zuwa
  • Maharaj Ji ya ce ya dace a bar yankin Kudu ya kammala wa’adin shekaru takwas kamar yadda Muhammadu Buhari daga Arewa ya yi mulki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Wanda ya kafa kungiyar One Love Family, Satguru Maharaj Ji ya yi magana game da takarar Atiku Abubakar a zaben 2027.

Malamin ya gargadi tsohon Mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar kan takarar zaben shekarar 2027 da ake tunkara a kasar.

An gargadi Atiku kan sake tsayaw takara a 2027
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar. Hoto: Atiku Abubakar.
Source: Facebook

An buƙaci Atiku Abubakar ya bar da takara

A cikin sanarwar da ya aikewa Tribune, Maharaj Ji ya ce bai kamata Atiku ko sauran ‘yan Arewa su tsaya takara ba a 2027.

Kara karanta wannan

Tinubu ya yi karin haske kan zargin shirin sauya sunan Najeriya, rusa shari'ar Musulunci

Ya bayyana cewa akwai yarjejeniyar siyasa tsakanin Arewa da Kudu wadda ta tsara yadda ake musayar mulki domin tabbatar da daidaito a Najeriya.

Maharaj Ji ya ce dole ne yankin Kudu ya kammala shekaru takwas a Aso Rock kamar yadda yankin Arewa ya yi lokacin mulkin Muhammadu Buhari.

Shawarar da Maharaj ya ba dattawan Arewa

Ya kara da cewa dattawan Arewa da sauran masu fada a ji su shawo kan Atiku da sauran masu neman takara su hakura.

Ya ce:

“Dole ne a bar Kudu ta kammala wa’adinta na shekaru takwas a Aso Rock kamar yadda Arewa ta yi a gwamnatin Buhari da ta gabata.”
An bukaci Atiku ya bar Tinubu ya kammala shekaru 8
Shugaba Bola Tinubu na Najeriya yana jawabi. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Source: Twitter

Matsalar da tsayawar Atiku takara za ta jawo

Jagoran addinin ya ce shirin sake tsayawar Atiku zai iya haddasa rikicin siyasa tare da kara dagula zaman lafiya kafin babban zaben 2027, cewar Daily Post.

Maharaj Ji ya zargi wasu manyan ‘yan Arewa da taimakawa wajen tabarbarewar matsalolin siyasa da tattalin arziki da Najeriya ke fuskanta yanzu.

Ya soki ci gaba da burin Atiku na neman shugabanci duk da cewa ya dade yana cin moriyar mukaman gwamnati a rayuwarsa.

Kara karanta wannan

Tinubu ya fadi tukwicin da zai saka wa 'yan Najeriya da shi idan ya koma Aso Villa

Gargadin da Maharaj ya yi kan takara a 2027

Maharaj Ji ya yi gargadi cewa duk wani mataki da zai kawo tangarda ga tsarin siyasar yanzu na iya haifar da tashin hankali mara amfani nan gaba.

Ya bukaci ‘yan Najeriya su rungumi zaman lafiya da biyayya ga kundin tsarin mulki domin kare hadin kai yayin shirye-shiryen babban zaben kasar wanda ake ganin zai yi zafi sosai.

An gargadi Jonathan kan takarar 2027

Mun ba ku labarin cewa an shawaci Goodluck Jonathan da kada ya nemi takarar kujerar shugaban ƙasa a 2027, duk da kiran da wasu magoya baya ke yi masa.

Primate Henry Chukwudum Ndukuba ne ya ba wa tsohon shugaban ƙasar wannan shawarar a wani taro da aka ɗauka a cikin wani bidiyo da ke yawo.

A cikin bidiyon, wanda ya fara haifar da martani daban-daban daga ’yan Najeriya, an hango tsohon shugaban ƙasar tare da wani tsohon shugaban Najeriya, Yakubu Gowon.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.