Guru Maharaji ya bukaci Buhari ya nada shi a matsayin mai bashi shawara domin ya jagoranci ma’aikatar man fetur da sauransu
Babban matsafi nan kuma Shugaban gidauniyar One Love Family, Sat Guru Maharaj ji, a ranar Talata, 4 ga watan Yuni yayi kira ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya nada shi a matsayin mai bashi shawara na tsarkin jiki.
Yace akwai bukatar hakan saboda sauran kungiyoyin addini da shuabanninsu sun gaza.
Maharaj ji ya gabatar da wannan bukata ne a lokacin wani taron manema labarai.
An gudanar da taron ne a kauyen Maharaj ji da ke hanyar babbar tikin Lagos/Ibadan.
Yace daga cikin abubuwan da ya ke sanya rai shine Shugaban kasar ya nada sa a matsayin wanda zai jagoranci ma’aikatun ruwa, noma, mai da gas a mulkin Buhari na biyu.
Baya ga neman a bashi mukami, matsafin ya kuma yi magana kan sauran lamura.
Yace gwamnatin tarayya na bukatar kara albashi sannan ta inganta jin dadin alkalai a kasar domin hana su karban cin hanci kai tsaye ko ta hannun wakilai.
KU KARANTA KUMA: Allah ya yiwa tsohon kwamishinan Kaduna, Abdulsalam Baba Ahmed rasuwa
Ya kuma yi kira ga samar da yan sandan jiha, cewa zai taimaka sosai wajen inganta lamarin tsaro a kasar.
Maharaj ji ya kuma shawarci gwamnatin tarayya da ta bayyana sunayen wadanda ke da hannu a almubazaranci da kudaden wasu kamfanonin da aka siyar a Najeriya, ciki harda na jiragen saman Najeriya, Ajaokuta Steel, Delta Steel, hukumar NEPA da saurasu.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Ga masu bukatar manhajar mu na Azumi a wannan wata mai albarka sai a bibiyi wannan shafi https://fb.gg/play/ramadan_ramadan
Asali: Legit.ng