2027: Birtaniya Ta Magantu kan Goyon Bayan Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a Najeriya
- Ƙasar Birtaniya ta yi magana musamman ame da zaben shugaban kasa a shekarar 2027 da ake tunkara a Najeriya da ake ganin zai yi zafi
- Jakadiyar Birtaniya a Najeriya, Gill Lever, ta ce gwamnatin Birtaniya ba ta da dan takara da ta fi so a zaben 2027 Najeriya da ke tafe
- Ta kara da cewa gwamnatin Birtaniya ba za ta tsoma baki a zabukan Najeriya ba, za ta goyi bayan sahihanci da zaman lafiya zabe
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Jakadiyar Birtaniya a Najeriya Gill Lever ta yi magana game da ɗan takarar shugaban kasa a zaben Najeriya da ake tunkara a 2027.
Lever ta ce gwamnatin Birtaniya ba ta da dan takara da ta fi so a zaben 2027 cikin dukan yan takarkari da dama da ake da su a kasar.

Source: Facebook
Ta bayyana hakan yayin ziyarar da ta kai Kwara inda ta gana da Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq a Ilorin, babban birnin jihar, cewar Channels TV.
Birtaniya ta fadi matsayarta kan zaben Najeriya
Ta kara da cewa gwamnatin Birtaniya ba za ta tsoma baki a harkar zaben Najeriya ba, tana goyon bayan sahihanci da zaman lafiya a zabe.
Ta ce Birtaniya za ta goyi bayan zabe mai zaman lafiya, sahihanci da sahihiyar wakilci a Najeriya ba tare da son rai ba ko kadan.
Ta ce gwamnatin Birtaniya tana da tsanani wuri yin taka tsan-tsan, ba ta son shiga cikin harkokin siyasar cikin gida ko nuna jam’iyya a Najeriya gaba ne.

Source: Facebook
Ci gaban da gwamnatin Kwara ta samar
Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya ce gwamnatinsa ta samu ci gaba a fannoni daban-daban na tattalin arziki da jin dadin jama’a a Kwara.
Ya ce an inganta ilimi da kiwon lafiya, an biya albashi, an kawar da bashin albashi da aka gada a jihar Kwara gaba ne.

Kara karanta wannan
"Ba dai a matsayin rauni ba," Gwamna Radda ya kafa sharadin sulhu da 'yan bindiga
Ya kara da cewa an fadada ilimin jami’a da kiwon lafiya ta hanyar gina cibiyoyin koyarwa biyu a Kwara a Najeriya gaba ne shi.
Ya ce gwamnatin Najeriya na karfafa noma, an kafa masana’antar sarrafa shea a Kaiama, za ta zama ta biyu mafi girma a Najeriya ne.
'Yadda aka inganta tsaro a Najeriya'
Gwamnan ya kuma yi bayani kan kokarin gwamnati wajen inganta tsaro da hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki a Kwara Najeriya gaba ne.
Ta kuma kai ziyara ga Uwargidan Gwamna Okufolake AbdulRazaq a ofishinta da ke Ilorin a jihar Kwara Najeriya gaba ne ziyarar ta gudana lafiya.
Birtaniya ta yi magana kan raba Najeriya
A wani labarin, an ji cewa gwamnatin Najeriya ta yi karin haske kan wata bukata da shugaban yan a ware, Sunday Igboho ya nema daga kasar Birtaniya.
A ranar Lahadi 14 ga watan Oktoban 2025, alshugaban yan a waren ya ce ya tura takarda ga firaministan Birtaniya kan neman ƙirƙiro kasar Yarabawa.
Gwamnatin kasar Birtaniya ta tabbatar da cewa ta karbi takardar da Sunday Igboho ya rubuta amma ta fadi matsayin wasikar da ta samu daga Igboho.
Asali: Legit.ng
