ADC: Tsohon Minista, Amaechi Ya Zama na 2 da Ya Sayi Fam na Takarar Shugaban Kasa a 2027

ADC: Tsohon Minista, Amaechi Ya Zama na 2 da Ya Sayi Fam na Takarar Shugaban Kasa a 2027

  • Rotimi Amaechi ya sayi fam din nuna sha'awa da shiga tseren neman takarar shugaban kasa a inuwar jam'iyyar adawa ta ADC
  • jigon ADC kuma shugaban kwamitin manufofi na jam’iyyar, Cif John Odigie-Oyegun, ne ya jagoranci tawagar da ta karbi fam a madadin Amaechi
  • Tsohon ministan ya sha bayyana cewa yana da gogewar da idan ya samu damar hawa mulki, zai warware matsalolin da suka addabi kasar

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya sayi fam ɗin nuna sha’awa da tsayawa takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar adawa ta ADC a shirye-shiryen tunkarar zaben 2027.

Babban jigon ADC kuma shugaban kwamitin manufofi da kundin tsarin jam’iyyar, Cif John Odigie-Oyegun, ne ya jagoranci wata tawaga zuwa sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja domin karɓar fom ɗin a madadin Amaechi.

Kara karanta wannan

Hayatudeen: Mai neman takarar shugaban kasa ya riga Atiku sayen fom din ADC, ya dauki alkawura

Rotimi Amaechi.
Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi yana jawabi ga magoya bayansa da suka fito tarbarsa a birnin Fatakwal na jihar Ribas Hoto: Chubuike Rotimi Amaechi
Source: Facebook

Amaechi ya sayi fam din takara a ADC

Sanata Abatemi-Usman na cikin tawagar da ta karɓi fom ɗin a ranar Juma’a, 8 ga watan Mayu, 2026, kamar yadda jaridar Tribune Nigeria ta ruwaito.

Amaechi dai ya taba rike kujerar kakakin majalisar dokokin Ribas da kuma gwamnan jihar na tsawon wa'adi biyu, kafin daga bisani a nada shi Ministan Sufuri a gwamnatin tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari.

Tsohon gwamnan ya shiga tseren neman takarar shugaban kasa ne bayan samun goyon baya daga sassa daban-daban, musamman shugabannin ADC daga yankin Kudu maso Kudu.

Mutum 2 sun karbi fam a ADC

Amaechi ya zama na biyu da ya sayi wannan fom na nuna sha'awar tsayawa takarar kujera lamba daya a jam'iyyar ADC, wanda kuɗinsa ya kai Naira miliyan 90.

Kafin shi, Alhaji Mohammed Hayatu-Deen ya riga ya sayi fom ɗin domin nuna aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin ADC a zaɓen 2027.

Kara karanta wannan

ADC ta dura kan Peter Obi, ta 'gano' manufarsa game da siyasar Najeriya

Amaechi ya sha bayyana cewa Najeriya na buƙatar shugabanci mai ƙwarewa tare da bai wa matasa dama da kuma ci gaba da tsarin karba-karba tsakanin yankunan kasar nan.

John Oyegun.
John Oyegun dauke da fam din takarar ADC da ya karba a madadin tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi Hoto: Anas Bello/Facebook
Source: Facebook

Amaechi ya shirya tunkarar matsaloli

Ya kuma ce tsaro, tattalin arziki da bunƙasa ababen more rayuwa su ne manyan abubuwan da ya kamata gwamnatin gaba ta mayar da hankali a kai domin gina gobe mak kyau ga yan Najeriya.

A cewarsa, gogewarsa a harkar mulki da ayyukan raya ƙasa sun isa shaidar da za ta nuna ya cancanci a ba shi dama a 2027 domin tinkarar matsalolin Najeriya, kamar yadda Vanguard ta kawo.

“Na san matsalolin ƙasar nan kuma ina da ƙwarewar da zan iya magance su,” in ji Amaechi.

Amaechi ya hango faduwar Tinubu a 2027

A wani labarin, kun ji cewa Rotimi Amaechi ya bayyana cewa ’yan Najeriya da dama suna ɗokin ganin sun kori Shugaba Bola Tinubu daga kan mulki a zaɓen shekara mai zuwa.

Amaechi ya bayyana tabarbarewar yanayin tattalin arziƙi da ƙaruwar wahalhalu a faɗin ƙasar a matsayin dalilan da za su sa yan Najeriya su maida Shugaba Tinubu gida a 2027.

Tsohon ministan sufurin ya kuma soki yadda ake amfani da ƙabilanci da addini a siyasa, yana mai nuna cewa hakan ya taimaka wajen kawo yanayin da ake ciki yanzu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262