'Mutuwa ce Kawai za Ta Raba Ni da APC,' Tarihi Ya Tuna Maganganun El Rufa'i

'Mutuwa ce Kawai za Ta Raba Ni da APC,' Tarihi Ya Tuna Maganganun El Rufa'i

  • Bayan ficewarsa daga APC, tarihi ya tono wasu maganganun El-Rufa'i da kalamansa na cewa ba zai taɓa barin jam’iyyar ba
  • A shekaru uku da suka wuce, tsohon gwamnan jihar Kaduna ya bayyana cewa APC tana cikin jerin abubuwan da ya ƙirƙira
  • A 2022, El-Rufa'i ya sha alwashin cewa idan ya bar APC, to hakan na nufin ya daina siyasa gaba ɗaya ba wata jam'iyya da zai koma

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Kaduna - Bayan ficewar tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufa'i daga jam’iyyar APC, an tuno kalamansa na baya, inda ya taɓa cewa ba zai taɓa barin APC ba har abada.

El-Rufa’i ya bayyana hakan ne a wata hira kai tsaye da aka watsa ta gidajen rediyon Kaduna a 2022, inda ya musanta jita-jitar cewa yana shirin sauya sheƙa daga APC.

Kara karanta wannan

Daga sauya sheka, El Rufa'i ya fadi yadda zai jawo rugujewar APC a Najeriya

Kaduna
Wasu maganganun El-Rufa'i kan fita daga APC a 2023. Hoto: Nasir El-Rufa'i
Asali: Facebook

Jaridar Leadership ta wallafa cewa tsohon gwamnan ya ce yana daga cikin mutum 37 da suka assasa jam’iyyar APC, don haka yana kallon jam’iyyar a matsayin ɗaya daga cikin ’ya’yansa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

2022: El-Rufa’i ya nuna amincewa da APC

A cikin tattaunawar da ya yi a 2022, El-Rufa’i ya ce babu wani dalili da zai sa ya bar APC, yana mai cewa:

“Lokacin da na bar APC, to hakan yana nufin na daina siyasa gaba ɗaya.”

A lokacin, tsohon gwamnan ya musanta rahoton da ke cewa ya cire tutar APC daga motarsa ta ofis, yana mai cewa dokar gwamnatin jiha ce a sauke tutoci bayan ƙarfe 6:00 na yamma.

Ya ce:

“Idan tuta tana a kan sandar gini, ana sauke ta bayan ƙarfe 6:00 na yamma. Idan kuma tana jikin mota, ana rufe ta. Wannan ba sabon abu ba ne.”

El-Rufa'i ya musanta sauya sheƙa a 2022

Kara karanta wannan

"Mai jiran gado": Martanin 'yan Najeriya bayan El Rufai ya fice daga APC zuwa SDP

A lokacin hirar, El-Rufa’i ya karyata ikirarin da ake yi cewa yana shirin sauya sheƙa zuwa wata jam’iyya saboda matsalar zaɓen mataimakin shugaban ƙasa a APC.

A cewarsa:

“Tun farko sun ce ina son zama shugaban ƙasa, daga baya suka ce ina son zama mataimaki, yanzu kuma sun dawo suna cewa ina son zama daraktan yaƙin neman zaɓe.”

A lokacin, El-Rufa'i ya kara da cewa ya ce irin waɗannan jita-jita ba su da tushe, kuma ana yinsu ne domin ɓata masa suna.

Elrufa'i
Lokacin da El-rufa'i ya ziyarci Atiku. Hoto: Atiku Abubakar
Asali: Facebook

Nasir El-Rufa'i ya fita daga APC a 2025

Bayan shekaru uku, El-Rufa’i ya fice daga APC, hakan yasa ake tambaya ko yana nufin ya sauya ra’ayin da ya bayyana a baya cewa ba zai bar jam’iyyar ba.

Baya ga hakan, an jiyo cewa tsohon gwamnan ya koma jam’iyyar SDP, yana mai cewa zai jagoranci ƙawancen jam’iyyun adawa domin fuskantar APC a 2027.

Kara karanta wannan

2027: An gano manyan dalilai 2 da suka sanya El Rufai ya bar APC, ya koma SDP

El-Rufa'i ya ziyarci Atiku Abubakar

A wani rahoton, kun ji cewa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa'i ya ziyarci Wazirin Adamawa watau Atiku Abubakar.

Tsohon gwamnan ya ziyarci Atiku Abubakar ne a gidansa kuma sun yi buda baki tare da wasu manyan 'yan siyasa a fadin kasar nan.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Wanda ya tantance Ibrahim Yusuf, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng

Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng