“An Kara Albashin Sanatoci, ‘Yan Majalisa Daga N13m da N21m Zuwa N8.5m da N13m”

“An Kara Albashin Sanatoci, ‘Yan Majalisa Daga N13m da N21m Zuwa N8.5m da N13m”

  • Ja’afar Ja’afar ya fito yana zargin cewa an yi wa duk wani ‘dan majalisar tarayya da sanata karin albashin da yake karba
  • ‘Dan jaridar ya fito yana ikirarin sanatan da ake biya N13.5m a kowane wata, yana tashi da sama da N20m a halin yanzu
  • Idan zancen Ja’afar gaskiya ce, ‘yan majalisar wakilan tarayyan kasar sun samu karin miliyoyin kudi a kan albashinsu

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Abuja - Fitaccen ‘dan jaridar nan, Ja’afar Ja’afar ya yi ikirarin an kara albashin da ‘yan majalisar tarayya suke karba.

Malam Ja’afar Ja’afar ya yi wannan magana ne a shafukansa na sada zumunta musamman a X da kuma Facebook.

Kara karanta wannan

Kungiyar malaman jami'o'i ta tsunduma yajin aiki kan matsalolin da take fuskanta

Majalisa
Ana zargin an kara albashin 'yan majalisa a Najeriya Hoto: @Dolusegun, @NgrSenate
Asali: Twitter

Ana jiran Tinubu ya kara albashin ma'aikata

‘Dan jaridar ya tada kuri’a, ya jawo ana ta tir da gwamnatin Bola Tinubu a lokacin da mutane ke jiran a kara albashin ma’aikata.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Da yake magana a dandalin X, Ja’afar ya ce idan za a cire tallafi ko kara kudin lantarki, farat daya ake yanke hukunci.

Amma idan ana bukatar karin albashi, ya ce sai a yi ta zaman kwamitoci barkatai har da yajin-aiki kafin a waiwayi ma’aikata.

"An kara albashin 'yan majalisa" - Ja'afar

“A karkashin shugaban kasa (Bola) Tinubu, kowane Sanata ya samu karin albashi daga N13.5m zuwa N21m a kowane wata
Kamar yadda albashin ‘yan majalisar wakilan tarayya ya karu daga N8.5, zuwa N13.5m.
Nawa ne sabon mafi karancin albashin da ma’aikatan gwamnati suke karba?”

- Ja'afar Ja'afar

Kara karanta wannan

Jerin gwamnonin da suka kara albashi ga ma'aikata a jihohinsu

Mutane sun soki 'karin' albashin 'yan majalisa

Fateema Muhammad Bawa ta ce:

"Taliya ce Sanadi"
“Allah Sarki talaka”

Inji Alhaji Muhammad Mardy

“Kai dai Nigeria sai dai mu ci gaba da addu'a.. amma wahalan ba ta misaltuwa”

- Kabir Easer

Auwal Ubangida Dunari yake cewa:

“Allah ya saka mana mun shiga hannun 'yan sari”

Auwal Salisu Isah yana mamakin ganin yadda gwamnatin tarayya ta gaza yanke N150, 000 a matsayin mafi karancin albashi.

Wani Malam Ghali ya ce:

"Abin takaici."

"A jihar Borno kuwa, wasu malaman N7500 su ke karba," a cewar Halilu Abdullahi.

Shi kuwa wani Prince D. Biechiey sai dai ya yi ta salati:

“Innalillahi wa inna ilaihi raji'un”

Nazifin Jarumi Rurum kuwa ya goyi bayan karin albashin, ya ce:

“Sune suke dawainiya da al'ummar, ai kudinmu wajensu yake komawa kacokan gaba daya, fatanmu Allah yakawo mana dauki”

Sanatoci da 'yan majalisa za su ci N50bn

Kara karanta wannan

Gwamnan APC ya tuna da ma'aikata bayan ya yi musu karin N10,000 a albashinsu

Rahoto ya zo a baya cewa albashi da alawus na duka ‘Yan majalisar Najeriya a tsawon shekaru hudu yana neman kai N50bn.

Nan da 2027, ‘Yan majalisar wakilai da Sanatocin tarayya za su raba Naira biliyan 32 tsakaninsu alhali ana biyan ma'aikata N30, 000.

Asali: Legit.ng

Online view pixel