Zance Ya Kare, INEC Ta Fara Dora Sakamakon Zaben Gwamnan Osun a Shafin IReV

Zance Ya Kare, INEC Ta Fara Dora Sakamakon Zaben Gwamnan Osun a Shafin IReV

  • Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC ta far dora sakamakon zaben gwamnan jihar Osun a shafinta na yanar gizo (IReV)
  • Bayanan da aka tattaro sun nuna cewa zuwa yanzu, INEC ta wallafa sakamakon rumfunan zaɓe 1,011 cikin 3,763 a shafinta na IReV
  • Sakamakon da aka dora a shafin INEC ya kai kashi 26.87 cikin 100 na jimillar sakamakon da ake jira daga rumfunan zaben Osun

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Osun, Nigeria - Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta fara dora sakamakon zaben gwamnan Osun a shafinta na tattara sakamako watau IReV.

Wannan na zuwa ne bayan an kammala kada kuri'u tare da kidaya wa a zaben gwamnan jihar Osun, wanda ya gudana yau Asabar, 15 ga watan Agusta, 2026.

Osun.
Masu yiwa kasa hidima suna aiki a zaben gwamnan Osun da hoton wani bangare na shafin IReV Hoto: INEC Nigeria
Source: Facebook

INEC ta fara dora sakamako a IReV

Kara karanta wannan

Wata sabuwa: Gwamna ya gano shirin da APC ta yi wajen tattara sakamakon zaben Osun

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa kawo yanzu, INEC ta wallafa sama da kashi 25 cikin 100 na sakamakon zaɓen gwamnan jihar Osun a shafinta na IReV.

An fara ɗoraa sakamakon ne jim kaɗan bayan kammala kaɗa ƙuri’a a rumfunan zaɓe da dama a faɗin jihar, bayan rufe lokacin kaɗa ƙuri’ar.

Tun farko dai, INEC ta sanya ƙarfe 2:30 na rana a matsayin lokacin rufe zaɓen a kowace mazaba.

Sakamakon rumfunan 1,011 ya bayyana

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, an ɗora sakamakon rumfunan zaɓe 1,011 cikin rumfunan 3,763 da ke jihar Osun a shafin IReV, kimanin kashi 26.87 cikin 100 na jimillar sakamakon da ake sa ran za a wallafa.

Sai dai a rahoton Daily Trust, INEC ta dora sakamakon rumfunan zabe 1,517 daga cikin jimillar 3,763, watau kashi 40.31 cikin ɗari.

Wannan ci gaba ya nuna fara tura sakamakon rumfunan zaɓe ta hanyar na’ura tare da bai wa jama’a damar kallon sakamakon yayin da jami’an zaɓe ke ci gaba da tattara sakamakon zaɓen.

Adeleke.
Gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke a wurin yakin neman zabe Hoto: @Adeleke01
Source: Facebook

IReV na ƙara bayyana gaskiya

Shafin IReV na bai wa jama’a da sauran masu ruwa da tsaki musamman masu sanya ido kan zabe damar duba sakamakon da aka wallafa daga rumfunan zaɓe.

Kara karanta wannan

Osun 2026: Muhimman abubuwa 8 da ya kamata kowane mai katin zabe ya sani

Hakan na taimakawa wajen ƙara nuna gaskiya a tsarin zaɓe yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon daga rumfunan zaɓe zuwa matakan da suka dace.

Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun na kokarin tazarce a kan mulki karkashin inuwar jam'iyyar Accord, yayin da yan takarar jam'iyyun hamayya ke yunkurin kayar da shi.

Gwamna Adeleke ya zargi APC

Kun ji cewa gwamnan Osun, Ademola Adeleke, ya zargi APC da shirin kai sakamakon zaɓe kai tsaye zuwa cibiyar tattarawa maimakon bin tsarinNda aka tanada.

Adeleke ya bayyana hakan ne jim kaɗan bayan ya jefa ƙuri’arsa a rumfar zaɓe ta 9, Ward 2, a ƙaramar hukumar Ede North.

A cewarsa, hakan zai kauce wa tsarin da ya kamata a bi daga rumfunan zaɓe zuwa mazabu sannan zuwa ƙananan hukumomi kafin a kaiBsakamakon cibiyar tattara sakamakon.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262