Jerin Gwamnonin da Suka Kara Albashi Ga Ma'aikata a Jihohinsu

Jerin Gwamnonin da Suka Kara Albashi Ga Ma'aikata a Jihohinsu

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Wasu gwamnonin jihohin Najeriya sun ƙara albashin ma'aikatan gwamnati a jihohinsu saboda tsadar rayuwa da ake fama da ita a ƙasar nan.

Ma’aikatan gwamnati a faɗin ƙasar nan sun yi ta kokawa domin samun ƙarin albashi saboda halin da tattalin ƙasar nan ya tsinci kansa a ciki.

Gwamnonin da suka yi karin albashi
Gwamna Godwin Obaseki da sauran gwamnoni 2 sa suka yi karin albashi Hoto: @FrancisNwifuru/@GovernorObaseki/@officialspbo
Asali: Twitter

Wasu daga cikin ma'aikatan kwalliya ta fara biyan kuɗin sabulu inda aka yi musu ƙarin albashi.

Gwamnonin da suka ƙara albashin ma'aikata

Ga jerin sunayen gwamnonin jihohin Najeriya da suka amsa kiran ma’aikata tare da ƙara musu albashi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Gwamna Godwin Obaseki na Edo

Na farko a jerin sunayen shine Gwamna Godwin Obaseki na jihar Edo. Obaseki ya sanar da sabon mafi ƙarancin albashi na N70,000 ga ma’aikatan jihar a ranar Litinin, 29 ga watan Afrilu.

Kara karanta wannan

Gwamnan APC ya tuna da ma'aikata bayan ya yi musu karin N10,000 a albashinsu

Sabon mafi ƙarancin albashin ma’aikatan jihar Edo ƙari ne daga N40,000 zuwa N70,000, cewar rahoton jaridar The Nation.

Gwamnan na jam’iyyar PDP ya ce a ranar Laraba 1 ga watan Mayu, 2024 ne ake sa ran za a fara biyan mafi ƙarancin albashin.

2. Gwamna Bassey Otu na Kuros Ribas

Gwamna Bassey Otu ya amince da sabon mafi ƙarancin albashi na N40,000 ga ma’aikatan gwamnati a jihar Kuros Ribas.

Gwamnan na jam’iyyar APC ya ce sabon tsarin albashin ya yi dai-dai da abin da jihar za ta iya biya, duba da yanayin kason da take samu daga gwamnatin tarayya, cewar rahoton jaridar Leadership.

Gwamna Bassey Otu ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da ba da fifiko wajen biyan albashi da kuɗaɗen fansho na ma’aikata.

3. Gwamna Francis Nwifuru na Ebonyi

Wani gwamnan APC da ya yi wa ma’aikatan gwamnati ƙarin albashi a jiharsa shi ne Gwamna Francis Nwifuru na jihar Ebonyi.

Kara karanta wannan

Tinubu ya amince da yi wa ma'aikata karin albashi, bayanai sun fito

Wannan ci gaban ya zo ne watanni takwas bayan gwamnan ya ƙara Naira 10,000 ga albashin ma’aikatan jihar Ebonyi a watan Yulin 2023.

Hakan dai ya kasance cika alƙawarin da gwamnan ya yi na ba da fifiko ga jin daɗin ma’aikatan jihar tare da ƙara haɓɓaka ayyukan ma’aikata.

Lokaci fara aikin sabon albashi

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnatin tarayya ta ce sabon mafi ƙarancin albashin ma’aikata a Najeriya zai fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Mayun 2024.

Gwamnatin ta ce ta yanke wannan hukuncin duk da cewa kwamitin da ke da alhakin ba da shawara kan ƙarin albashin ma'aikata bai gabatar da rahotansa ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel