Dalilin da Ya Sa Muka Gayyaci Nasir El-Rufai Zuwa Borno Inji Gwamnatin Zulum
- Gwamnatin jihar Borno ta tabbatar da gayyatar tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai
- Mai bawa gwamnan shawara ce, Fatima Muhammad Abbas, ta bayyana dalilan gayyatar tsohon gwamnan Kadunan a shafinta na X.
- A wurin taron, Malam Nasir El-Rufai ya yi wasu jawabai masu kama da martani wa magajinsa, Sanata Uba Sani.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Ziyarar da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai ya kai jihar Borno ta jawo ka-ce-na-ce.
Hakan ya biyo bayan ziyarce-ziyarcen da ya kai ne ga wasu 'yan jam'iyyar adawa wanda har hakan ya kai ga hasashen cewa yana shirin chanja sheƙa.
![El-Rufai El-Rufai](https://cdn.legit.ng/images/1120/46688af825c7f009.jpeg?v=1)
Asali: Twitter
Amma a na ta bangaren, gwamnatin jihar Borno ta bayyana dalilai da suka sa ta gayyaci tsohon gwamnan jihar Kadunan, wanda ta bayyana cewa ziyarar bata da alaka da siyasa
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/03a575e126f84401.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Tsohon gwamna Malam El-Rufa'i ya bayyana babbar matsala 1 tak da ta addabi Najeriya
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Dalilin gayyatar El-Rufai Borno
Mai bawa gwamnan shawara ce, Fatima Muhammad Abbas, ta bayyana dalilan a shafinta na X.
Ta bayyana cewa gwamnatin ne da kanta ta gayyace shi domin ya gabatar da takarda a wurin horo na musamman.
Gwamnatin Babagana Umara Zulum ta yi wa ma'aikata horo ne a kan kwarewa wurin zartar da aikace-aikacen gwamnati.
El-Rufai ya yi martani wa Uba Sani
A kwanakin baya dai gwamna Uba Sani ya zargi El-Rufai da barin tarin bashi a jihar Kaduna, wanda hakan ke kokarin hana ayyukan raya kasa a fadin jihar.
Tsohon gwamnan jihar Kadunan ya yi wani zance mai kama da martani wa magajin nasa, Uba Sani, a wurin taron. Ga abinda ya ce kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito:
"Ba na son zama ubangida, shi ya sa ba na tsoma baki a cikin abin da ke faruwa a Kaduna, ina son shi (gwamnan) ya koyi aikin da kansa."
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/e5997ce9a7a1e1f0.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
"Ban son zama ubangida" Malam El-Rufa'i ya mayar da martani kan abin da ke faruwa a Kaduna
"Ya kamata shugaba ya samu mutanen kirki da za suyi aiki tare. Allah ne kadai zai iya yin komai shi kadai, komai nagartar ka a matsayinka na shugaba, za ka zama ne kamar mutanen da ke kusa da kai, shi ya sa ake cewa gwargwadon nagartar ma'aikatan gwamnatinku, gwargwadon yadda za ku cigaba.”
- Nasir El-Rufai
El-Rufai ya ziyarci sanatan PDP
A wani rahoton kuma, kun ji cewa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya kai ziyara gidan Sanata Abdul Ningi, wanda majalisar dattawa ta dakatar kwanan nan.
Majalisa ta dakatar da Sanata Ningi, mamban jam'iyyar PDP mai wakiltar Bauchi ta Tsakiya saboda zargin cushe a kasafin kuɗin 2024
Asali: Legit.ng