Kotun Koli Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Karshe Kan Zaben Gwamnan APC, Komai Na Iya Faruwa

Kotun Koli Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Karshe Kan Zaben Gwamnan APC, Komai Na Iya Faruwa

  • Kotun Koli ta shirya raba gardama kan shari'ar zaben gwamnan jihar Sokoto da ake takaddama a kai
  • Kotun ta sanya yau Alhamis 25 ga watan Janairu don yanke hukuncin karshe kan shari'ar zaben gwamnan
  • A baya, Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Ahmad Aliyu na APC a matsayin gwamnan jihar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Sokoto - Jam'iyyun PDP da APC a jihar Sokoto na cikin zullumi yayin da suke dakon hukuncin Kotun Koli.

Kotun Koli ta shirya yanke hukuncin shari'ar zaben gwamnan jihar a yau Alhamis 25 ga watan Janairu, cewar Punch.

Kotun Koli za ta raba gardama a shari'ar zaben gwamnan jihar Sokoto
Kotun Koli Ta Shirya Yanke Hukuncin Karshe a Shari'ar Zaben Sokoto. Hoto: Ahmad Aliyu.
Asali: Twitter

Wane hukunci aka yi a baya?

Idan ba manta ba, Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Ahmad Aliyu na APC a matsayin zababben gwamnan jihar.

Kara karanta wannan

PDP vs APC: Kotun Koli ta yanke hukuncin karshe kan shari'ar gwamnan jihar Sokoto

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yayin ta yi watsi da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP, Sa'idu Umar saboda rashin gamsassun hujjoji, cewar Channels TV.

Daga bisani, Umar ya durfafi Kotun Koli don neman hakkinsa da aka kwace a Kotun Daukaka Kara.

Mambobin jam'iyyun APC da PDP a jihar sun nuna kwarin gwiwarsu ka wannan hukunci da za a yanke.

Martanin PDP da APC Kan shari'ar

Sakataren yada labaran PDP, Hassan Sentimental ya bayyana cewa su na da kwarin gwiwar samun nasara a kotun.

Ya ce:

"Muna da kwarin gwiwar samun nasara kotun a ranar Alhamis saboda hujjojin da muka gabatar.
"Sa yardar Allah madaukakin Sarki za mu samu adalci a kotun da za ta yanke hukunci."

Sai dai shugaban jam'iyyar APC a jihar, Isa Achida bai ce komai ba game da shari'ar da za a yanke a yau.

Kara karanta wannan

Kotun Koli ta sake yanke hukuncin karshe kan shari'ar neman kifar da gwamnan Kebbi

Ya ce bai kamata ya ce wani abu ba kan shari'ar da za a karkare ta ranar Alhamis, cewar Lagos Post Online.

Ya ce:

"Babu abin da zan iya cewa a kai a yanzu, shari'ar ta na gaban kotu kuma a gobe za a yanke ta, gaskiya ba zan iya cewa komai ba."

Kotu ta yi hukunci kan matsalar Majalisar Plateau

A wani labarin, Babbar Kotun Tarayya ta yi hukunci kan shari'ar Majalisar jihar Plateau a Najeriya.

Kotun ta ce ba za ta tilasta kakakin Majalisar dakatar da sabbin 'yan Majalisun APC 16 ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel