Abba Gida-Gida, Zulum da Sauran 'Yan takara 6 Masu Yawan Kuri'u a Zaben Gwamna

Abba Gida-Gida, Zulum da Sauran 'Yan takara 6 Masu Yawan Kuri'u a Zaben Gwamna

  1. New Nigeria Peoples Party, NNPP ta yi galaba a zaben Kano da kuri’un da sun zarce miliyan guda
  2. Akwai ‘Yan takaran All Progressive Congress da suka lashe zabe da ratar 300, 000 zuwa 400, 000
  3. Mun tattaro ‘yan takaran da suke da kuri’u masu yawa ko kuma akalla suka bada rata sosai a 2023

1. Abba Kabir Yusuf

Abba Kabir Yusuf da ya yi takara a karkashin jam’iyyar adawa ta NNPP ne kurum wanda ya samu kuri’u fiye da miliyan guda a zaben Gwamna da aka yi.

Zababben Gwamnan na Kano ya yi galaba a kan Nasiru Yusuf Gawuna da kuri’u 1,019,602, jam’iyyar APC da ta zo ta biyu ta na da kuri’u 890,705.

2. Babajide Sanwo Olu

A zaben Gwamnan Legas, Babajide Sanwo-Olu ya yi galaba a jam’iyyar APC, yana da kuri’u 762,134, shi kuwa Gbadebo Rhodes-Vivour ya samu 312,329.

Kara karanta wannan

Shekarau da Jiga-Jigan 'Yan siyasa 8 da Suka Tafka Asara 10 da 20 a Zaben Bana

Ko da kuri’u 450, 000 ne ratar ‘yan takaran biyu, mutum 62,449 sun zabi jam’iyyar PDP a Legas.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

3. Umaru Dikko Radda

Dr. Umaru Dikko Radda ya zama zababben Gwamnan Katsina ne da kuri’u 859, 892 a jam’iyyar APC. Yakubu Lado Danmarke na PDP yana da 486, 620.

Wannan rata ta kuri’a 370, 000 ta ba APC damar yin shekaru 12 ta na kan mulki a jihar Katsina.

4. Babagana Umar Zulum

Farfesa Babagana Umara Zulum zai zarce a kan kujerar Gwamnan jihar Borno a sakamakon gagarumar nasarar da ya samu a kan Mohammed Jajari.

Mai girma Gwamnan yana da kuri’u 545,543 shi kuwa ‘dan takaran PDP ya kare da 82,147. Tsakaninsu akwai tazarar fiye da kuri’u 460, 000 a zaben.

Zaben Gwamna
Abba, Sanwo Olu, Zulum, Radda Hoto: dpmnewsnigeria.com, dclhausa.com, guardian.ng
Asali: UGC

5. Seyi Makinde

Gwamnan Seyi Makinde yana cikin wadana suka ba abokan hamayyarsu tazarar raba-ni-da-yaro a 2023. Kuri’un PDP sun kusa ribanya na APC.

Kara karanta wannan

Duk da Guguwar Peter Obi, Jam’iyyar LP Ta Gaza Samun Gwamna ko 1 a Zaben Jihohi

Kuri’un Jam’iyyar PDP a takarar Gwamna sun kai 563,756 alhali ‘dan takaran da APC ta tsaida, Sanata Tai Folarin yana baya da kuri’u 260, 000 a zaben.

6. Umar Namadi

A zaben sabon Gwamnan jihar Jigawa, Jam’iyyar APC ta tabbata ta bada ratar kuri’u 256,685, kuma tayi nasara a kananan hukumomi 26 da ake da su.

Mustapha Sule Lamido da PDP ta tsaida ya yi nasara ne a Birnin Kudu kadai, ya samu 368, 726, Umar Namadi ya ci zabe da 618, 449, NNPP ta zo ta uku.

7. Bala Mohammed

INEC ta tabbatar da nasarar Bala Mohammed a zaben Gwamnan Bauchi a sakamakon kuri’u 525,280 da jam’iyyar PDP ta tashi da su a ranar Asabar.

Sadique Abubakar da ya tsaya a jam’iyyar APC ya zo na biyu a zaben, yana a kuri’u 432,272.

8. Caleb Muftwang

Da kuri’un da ba su haura 43,899 ba jam’iyyar PDP ta lashe zaben Jihar Filato a 2023. Barista Caleb Muftwang ya doke ‘dan takaran APC mai mulki.

Kara karanta wannan

Wasu ‘Yan Takaran APC Za Su Kotu Domin Karbe Nasarar PDP a Zaben Gwamnoni

Gaba daya Caleb Muftwang yana da kuri’a 525, 299, Farfesa Nentawe Yiltwada ya samu 481 370.

'Yan biyu babu a 2023

A rahotonmu kun ji yadda Yakubu Dogara ya ji kunya a zaben Shugaban kasa a PDP, sannan ya kunyata a zaben Gwamnan Bauchi da ya tsallaka APC.

Darektan yakin zaben Atiku Abubakar, Aminu Waziri Tambuwal da irinsu Sule Lamido su na kallo APC ta lallasa PDP a duka zabukan da aka yi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel