Duk da Guguwar Peter Obi, Jam’iyyar LP Ta Gaza Samun Gwamna ko 1 a Zaben Jihohi

Duk da Guguwar Peter Obi, Jam’iyyar LP Ta Gaza Samun Gwamna ko 1 a Zaben Jihohi

  • Har yanzu babu wata Jihar Najeriya da LP ta samu nasara a zaben Gwamnonin jihohi da aka yi
  • Jam’iyyar LP ta zo ta uku da kuri’u miliyan 6 a zaben shugaban kasa, yanzu lamarin ya canza
  • ‘Yan takaran Gwamnonin da LP ta tsaida ba su yi irin kokarin da Peter Obi ya yi a Fubrairu ba

Abuja - Kusan abin da magoya bayan Peter Obi da ake kira ‘Obidients’su ka yi tunani ba shi ya faru a zaben Gwamnonin jihohi da aka shirya ba.

A wani rahoto da Vanguard ta fitar, an ji yadda Jam’iyyar Labour Party ta gagara yin nasara a ko da Jiha guda ganin kokarinta a zaben shugaban kasa.

Har a yankin Kudu maso gabas da jam’iyyar hamayyar da ‘dan takaranta a 2023 watau Peter Obi suka doke APC da PDP, ba su tabuka abin a yaba ba.

Kara karanta wannan

2023: Jerin Jihohin da Ba'a Kammala Zaben Gwamna Ba da Waɗanda INEC Ta Dakatar da Tattara Sakamako

Idan aka yi la’akari da sakamakon INEC, har zuwa yanzu, babu LP a jerin jam’iyyun da suka lashe zaben Gwamna ko akalla su ke rike da mulkin jihar.

An san sakamakon Jihohi 24

Hukumar zabe na kasa ta sanar da sakamakon Jihohi 24 a cikin 28 da aka yi takara. Jam’iyyar APC na da jihohi 15, PDP ta samu 8, NNPP kuwa daya.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Jam’iyyar NNPP wanda ta zo na hudu a zaben shugaban kasa ta iya samun mulki a jihar Kano, mahaifar ‘dan takaranta, Rabiu Musa Kwankwaso.

Peter Obi
Peter Obi da Yusuf Datti Ahmed Hoto: @PeterObi
Asali: Twitter

Amma ‘Yan Obidients za su sa rai abubuwa su canza musamman ganin akwai jihohi biyu (watau Adamawa da Kebbi) da ba a kammala zaben ba tukuna.

Akwai rai a Abia da Enugu

Rahoton ya ce LP ta na burin kai labari a Abia da Enugu inda aka dakatar da tattara kuri’u, musamman ganin jihohin su na inda jam’iyyar ke da karfi.

Kara karanta wannan

Wasu ‘Yan Takaran APC Za Su Kotu Domin Karbe Nasarar PDP a Zaben Gwamnoni

An fi yi wa jam’iyyar ta su Peter Obi hangen nasara a wadannan jihohi biyu domin ana ganin ‘dan takararta ko na PDP zai zama sabon Gwamna a Mayu.

A jihohin Arewa da Obi ya samu kuri’u masu yawa a zaben shugaban kasa na watan Fubrairu, LP ba ta iya kamanta nasararta a takarar Gwamnoni ba.

A zaben na ranar Asabar, APC da PDP ne suka yi galaba a Filato da Nasarawa. Ba a batun LP a Kuros Riba, Delta, Ebonyi sai a Legas ne ta zo ta biyu.

Fayose da Tambuwal

An samu labari cewa Ayo Fayose ya yi matukar murna da faduwar ‘dan takaran Aminu Tambuwal a zaben sabon Gwamnan jihar Sokoto na 2023.

Fayose yake cewa Aminu Tambuwal ya ci amanar PDP da Asiwaju Tinubu, sannan ya ci amanar Nyesom Wike da ya mara masa baya a zaben 2019.

Kara karanta wannan

Tsohon Gwamnan PDP Ya Kwankwadi Giya Saboda Murnar Tambuwal Ya Kunyata a Sokoto

Asali: Legit.ng

Online view pixel