A Karon Farko a Shekara 24, PDP tayi Nasara a Zamfara, Gwamnan APC Ya Rasa Tazarce

A Karon Farko a Shekara 24, PDP tayi Nasara a Zamfara, Gwamnan APC Ya Rasa Tazarce

  • Gwamna Bello Matawalle ba zai zarce a kujerarsa ba, ‘Dan takaran PDP ya doke shi
  • Hukumar INEC ta tabbatar da cewa Lawal Dare ne zababben Gwamna a Zamfara a 2023
  • Duk da ta yi mulki a baya, amma wannan ne karon farko da PDP ta lashe zabe a jihar

Zamfara - Rahotanni sun tabbatar da cewa Lawal Dare ya doke Bello Matawalle a zaben Gwamnan jihar Zamfara da aka shirya.

Mai girma Gwamna Bello Muhammad Matawalle ya rasa tazarce a hannun ‘dan takaran jam’iyyar adawa ta PDP, Lawal Dare.

Daily Trust ta ce Alhaji Lawal Dare ya samu kuri’u 377,726 a zaben da aka shirya, Bello Mohammed Matawalle yana da 311, 976.

Baturen zaben Gwamnan jihar Zamfara, Farfesa Kasimu Shehu ya sanar da Lawal Dare a matsayin wanda ya yi nasara a takarar.

Kara karanta wannan

Wasu ‘Yan Takaran APC Za Su Kotu Domin Karbe Nasarar PDP a Zaben Gwamnoni

Jam'iyyar PDP ta ba APC rata

An samu ratar kuri’u 65, 800 tsakanin jam’iyyar PDP mai adawa da kuma APC mai mulki.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Legit.ng Hausa ta fahimci jam’iyyar APC tayi nasara ne a kananan hukumomin Bakura, Birnin Magaji, Mafara da Muradun.

Matawalle
Bello Mohammed Matawalle lokacin da ya bar PDP Hoto: premiumtimesng.com
Asali: UGC

PDP kuwa ta samu nasara a sauran kananan hukumomin Anka, Bukuyum, Bungudu, Gumi, Gusau, Kaura, Maru, sai Shinkafi.

Haka zalika ‘dan takaran PDP watau Lawal Dare ya doke Gwamna mai mulki a Tsafe da Zurmi.

PDP ta taba cin Zamfara?

Wannan ne karon farko da jam’iyyar PDP ta lashe zaben Gwamna a jihar Zamfara tun 1999, duk da tayi mulki sau biyu a jihar.

PDP aka ba nasara a zaben 2019 a dalilin sabawa dokar zabe da APC tayi. A wancan lokaci Jam’iyyar PDP ta zo na biyu ne.

Sannan Zamfara ta taba zama karkashin PDP a lokacin da Mahmuda Aliyu Shinkafi ya sauya-sheka, ya rasa tazarce a 2007.

Kara karanta wannan

Tsohon Gwamnan PDP Ya Kwankwadi Giya Saboda Murnar Tambuwal Ya Kunyata a Sokoto

Zaben jihar Kebbi

A zaben Gwamnan Kebbi, an ji labari jam’iyyar APC ta na da 388,258 sai PDP ta samu kuri’u 342,980, babu wanda ya yi nasara.

Dalili kuwa shi ne INEC ta ce a yayin da ake tattara sakamako, an soke adadin kuri’u 91, 829 daga kananan hukumomi har 20

Asali: Legit.ng

Online view pixel