Sabon Hasashe Ya Nuna Yadda Takarar 2023 Za Ta Kare Tsakanin APC, PDP, NNPP da LP

Sabon Hasashe Ya Nuna Yadda Takarar 2023 Za Ta Kare Tsakanin APC, PDP, NNPP da LP

  • Kamfanin Nextier ya yi hasashe a kan yadda mutane za su zabi ‘yan takaran shugaban kasa a 2023
  • Mafi yawan mutanen da aka zauna da su sun ce Peter Obi na jam’iyyar adawa ta LP za su zaba a badi
  • An cire Jihohin Legas, Adamawa, Anambra da Kano – inda ‘yan takaran suka fito, a wajen binciken

Abuja - Idan hasashen da kamfanin Nextier suka shirya ya tabbata gaskiya, Peter Obi ne zai zama sabon shugaban kasar Najeriya a Mayun shekarar 2023.

Hasashen Nextier ya nuna jam’iyyar LP za tayi galaba a zaben shugaban kasa da za ayi a Najeriya. Premium Times ta fitar da wannan rahoto a ranar Litinin.

An gudanar da wannan bincike ne ta hanyar tattaunawa da mutum 2, 000 da za suyi zaben shugaban kasa daga jihohi 12 da ake da su a shiyyoyin kasar nan.

Kara karanta wannan

Kwankwaso: Inda aka Samu Cikas, Maganar Taron Dangi da Peter Obi Ta Wargaje

Nextier sun ce ba suyi amfani da jihohin da ‘yan takaran suka fito a wajen binciken na su ba. A karshe aka fahimci APC, PDP da kuma LP ne suke kan gaba.

Ba a maganar NNPP a 2023?

Abin da binciken ya nuna shi ne ‘dan takaran NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso ba zai zo a sahun farko ba, duk da yana da goyon baya a Arewa maso yamma.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Rahoton da The Guardian ta fitar a makon nan ya nuna Obi yana da rinjayen goyon baya a kauyuka da kuri’u 40.37%, PDP da APC na biye da 26.7% da 20.47%.

A karshe 30% sun nuna LP za su zaba a 2023, Atiku Abubakar ya samu 17.3%, shi kuma Bola Tinubu yana da 4.98% sai Rabiu Kwankwaso ya kare da -8.70%.

Kara karanta wannan

Alkawuran Atiku: Zan yiwa Arewa aiki kamar Abubakar Tafawa Balewa idan na gaji Buhari a 2023

Peter Obi
'Dan takaran LP, Peter Obi Hoto: @PeterObo
Asali: Twitter

Atiku Abubakar da Tinubu sun fi farin jini a wajen mutanen da ba suyi karatun boko ba. Mafi yawan musulman da aka yi magana da su sun ce za su zabi PDP.

Yadda za ayi zabe a kowace shiyya

Kamfanin yace hasashensa ya nuna masa kusan 60% na mutanen Benuwai da Nasarawa a Arewa maso tsakiya za su zabi LP, PDP da APC za su raba 35%.

A Arewa maso gabas, Atiku yake gaba da 50.3% sai jam’iyyar APC mai-mulki a baya da 27.2%, NNPP ta tashi da 14.6% na kuri’un yayin da Obi ya samu 5.8% rak.

A jihohin Kudu maso Kudu, LP ta samu 67% na kuri’in da aka kada, PDP da APC sun samu 11% da 10.7%. A yankin Kudu maso gabas kuwa LP tana da har 94%.

A shiyyar Kudu maso yamma, 37.4% sun karkata ga Tinubu, Obi ya samu 24%, Atiku yana da 16.5%, sai Sanata Kwankwaso da NNPP suka tsira da 2.3% kacal.

Kara karanta wannan

Binciken ‘Yan Sanda Ya Nuna Jihohi 2 da Za a fi Samun Tashin Hankali a Zaben 2023

Hadin-gwiwar LP/NNPP

An samu rahoto da Rabiu Musa Kwankwaso ya yi bayanin zaman da aka yi tsakanin bangaren jam’iyyar NNPP da LP da inda aka ci karo da tasgaro a tattaunawar.

Jam’iyyun biyu sun yi niyyar dunkulewa ta yadda Kwankwaso zai hada-kai da Peter Obi saboda a lashe zabe amma dai hakan ya faskara saboda rashin jituwa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel