Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, zai ziyarci kasar Amurka. Atiku Abubakar zai je Amurka ne domin tattauna matsalolin da suka addabi Najeriya.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, zai ziyarci kasar Amurka. Atiku Abubakar zai je Amurka ne domin tattauna matsalolin da suka addabi Najeriya.
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda ya nuna alhini kan rasuwar fitaccen mawakin gargajiyar Hausa, Alhaji Surajo Mai-Asharalle, wanda ya rasu bayan fama da jinya.
Tsohon mataimakin sakataren yaɗa labaran jam'iyyar APC na ƙasa, Timi Frank ya shawarci kungiyar ƙwadago ta NLC kada ka karɓi tayin da bai kai ₦250,000 ba.
Gwamnatin tarayya ta ce ta kammala daukan mataki domin magance matsalolin da Najeriya ke fuskanta. Sakataren Gwamnatin, George Akume ne ya fadi haka.
Yan bindiga sun kai hari jihohin Zamfara da Katsina inda suka kashe mutane kimanin 50. Kwamishinan yan sandan jihar Zamfara ya tabbatar da faruwar lamarin.
Yayin da gwamnatin tarayya ta ja daga da gwamnatocin jihohi kan bawa ƙananan hukumomi 'yancin gashin kai, kungiyar ma'aikatan ƙananan hukumomi ta yi zanga zanga.
Wata kotu da ke zamanta a Abuja ta ci tarar kamfanin Multichoice na DSTV da GOtv N150m bayan kara kudi ga kwastomomi ba bisa ka'ida ba a Najeriya.
Wani kudirin doka da ke neman kafa wata jiha a shiyyar Kudu maso Gabas ya tsallake karatu na farko a zauren majalisar wakilai. Za a rika kiran ta da 'Jihar Orlu'.
Rahotanni sun nuna cewa kwamitin mafi ƙarancin albashi ya koma teburin ci gaba da tattaumawa kan sabon albashin ma'aikata, ana tsammanin yau ne zaman ƙarshe.
Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da fara gina titin karkara mai nisan kilomita 7.2 daga Mil Goma zuwa 'Yankatsari, da kilo mita 7.5 a Rijiyar Gwangwan kan N2.6bn.
Ministan kudi da harkokin tattalin arziki, Wale Edun, ya ce ba wani abun damuwa game da sabon mafi karancin albashi, ya gana da shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.
Labarai
Samu kari