Wasu Malaman Musulunci Sun Fada Tarkon Yan Bindiga a Hanyar Dawowa daga Taron APC

Wasu Malaman Musulunci Sun Fada Tarkon Yan Bindiga a Hanyar Dawowa daga Taron APC

  • Rahotanni daga Zamfara sun ce ‘yan bindiga sun sace wasu malaman addinin Musulunci bayan sun dawow daga gidan Sanata Abdul’aziz Abubakar Yari
  • Bayanai sun nuna cewa Malaman sun je gidan tsohon gwamnan Zamfara da ke Talaka Mafara ne domin halartar taron addu’a
  • An ce malaman sun fito ne daga ƙananan hukumomin Bakura da Talata Mafara kuma sun fada tarkon yan bindiga ne a hanyar komawa gida

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Zamfara, Nigeria - Rahotannin da ke shigowa daga Zamfara sun ce ‘yan bindiga sun sace wasu malaman addinin Musulunci da aka gayyata zuwa gidan Sanata Abdul’aziz Abubakar Yari.

An ruwaito cewa an gayyaci malaman zuws gidan Sanata Yarinda ke Talata Mafara a yau, Asabar, 12 ga Satumba, 2026 domin yin addu'a da godiya bisa nada shi Daraktan yakin neman zaben shugaban kasa na APC.

Kara karanta wannan

An fara fito da abubuwan da Tinubu ya shirya yi a Najeriya idan ya lashe zaben 2027

Malamai.
Malaman addinin musulunci a taron da Sanata Abdulaziz Yari ya shirya a gidansa da ke Zamfara Hoto: @Danbakatsina50
Source: Twitter

Wani mai amfani da shafin X wanda ke yawan kawo labaran da suka shafi matsalar tsaro a sassan Najeriya, Bakatsina ya tabbatar da aukuwar lamarim a wani sako da ya wallafa.

Sunayen wasu malamai da aka sace

Rahotannin sun ce malaman da aka ruwaisto cews yan bindiga sun sace sun haɗa da:

  • Limamin Juma’a na farko a masallacin Dogon Madacci, Imam Yahuza
  • Magawata Abdullahi, limamin Juma’a na biyu, Dogon Madacci
  • Malam Shehu Dakko
  • Imam Bala Fagon
  • Na’ibi Tasi’u, Tungar Nagudai

An ce malaman sun kasance a gidan Sanata Yari ne domin halartar taron addu’a. Sun fito ne daga wasu garuruwa da kauyuka da ke ƙananan hukumomin Bakura da Talata Mafara.

Lamarin ya jefa mutane cikin matuƙar damuwa, musamman ganin cewa rahotanni sun ce an sace malaman ne yayin da suka je gidan Sanata Yari, tsohon gwamnan Zamfara, kuma Darakta-Janar na yaƙin neman zaɓen Shugaba Bola Ahmed Tinubu na 2027.

Kara karanta wannan

Melaye ya yi gagarumin gargadi ga Tinubu idan EFCC ta kuskura ta cafke Atiku

A daidai lokacin da matsalar tsaro ke ƙara jefa al’ummomi a faɗin Zamfara cikin mawuyacin hali, wannan lamari ya sake haifar da tambayoyi masu tsanani kan tsaron jama’a a wuraren taruwar mutane.

Ana ganin dai idan har ana iya sace mutane yayin da suke halartar taro a gidan wani fitaccen ɗan siyasa, to ina ne talakawa za su ji cewa suna cikin aminci?

Karin bayani na tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262