'Ban Taɓa Fitar da Zakkah ba': Sarkin Zazzau Ya Faɗi Abin da Ya Fi ba Muhimmanci

'Ban Taɓa Fitar da Zakkah ba': Sarkin Zazzau Ya Faɗi Abin da Ya Fi ba Muhimmanci

  • Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli, ya ce bai taba tara isasshen kuɗin da zai cika sharuddan fitar da zakka ba
  • Bamalli ya bayyana cewa tara dukiya ba ta cikin abubuwan da yake bai wa muhimmanci, yana mai cewa shugabanci hidima ne ga al’umma
  • Sarkin ya ce burinsa shi ne a tuna da shi a matsayin shugaba mai adalci, ba saboda dukiya, matsayi ko abubuwan duniya ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Zaria, Kaduna - Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmed Nuhu Bamalli, ya ce a rayuwarsa bai taba tara isasshen kuɗin da zai sa ya zama wajibi ya fitar da zakka ba.

Zakka na daga cikin rukunan Musulunci guda biyar, kuma wajibi ne a fitar da ita daga dukiyar da ta kai adadin Nisabi, tare da cika sauran sharudda.

Sarkin Zazzau ya fadi yadda yake gudun tara dukiya
Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambassada Nuhu Bamalli. Hoto: Masarautar Zazzau Juya da Yau.
Source: Facebook

Bamalli ya ce ajiyarsa ta kashin kansa ba ta taba kaiwa matakin da zai wajabta masa fitar da zakka ta kuɗi ba, cewar Daily Trust.

Kara karanta wannan

Sarki Bamalli ya karyata cewa alakar jini ta jawo El Rufai ya nada shi Sarkin Zazzau

Ga kuɗaɗen da aka tara, adadin zakka da aka fi amfani da shi shi ne kashi 2.5 cikin 100, idan dukiyar ta kai Nisabi kuma ta shekara ta wata.

Sai dai darajar Nisabi tana sauyawa bisa farashin zinariya ko azurfa da kuma tsarin da malamai suka bi wajen ƙididdigawa.

A watan Satumbar 2026, darajar Nisabin zakka a Najeriya tana sauyawa kullum bisa farashin kasuwa, inda Nisabin zinariya ya kai kusan N15,654,875.

Nisabin azurfa kuwa ya kai kusan N1,722,571, bisa alkaluman da aka bibiyar a baya-bayan nan.

Sarkin ya ce haka yake rayuwa, yana mai cewa yana cikin kwanciyar hankali da irin wannan tsarin rayuwa da ya ɗauka game da dukiyarsa.

Ya ce:

“Ban taba fitar da zakka ta kuɗi a rayuwata ba, saboda ban taba tara kuɗin da zai kai tsawon lokacin da ake bukata domin fitar da zakka ba."
Da aka tambaye shi ya ƙara fayyace cewa bai taba fitar da zakka ba, sai Sarkin ya ce: “Ban taba tara isasshen kuɗi ba.”
“Eh, haka nake rayuwa. Ban taba yin hakan ba. Kuma ina rayuwa cikin kwanciyar hankali."

Kara karanta wannan

Yadda Kwankwaso zai ragargaji Atiku da Tinubu a zaben 2027 a Kano

Sarkin ya bayyana hakan ne a wata hira da Weekend Trust, gabanin cikar shekaru shida da hawansa kan gadon sarautar Zazzau.

A cewarsa, tarbiyyar da ya samu ita ma ta yi tasiri kan yadda yake kallon dukiya, yana mai cewa mahaifinsa ya bar N11,000 da tufafi guda biyar bayan rasuwarsa.

Bamalli ya kuma musanta zargin cewa ya tara kuɗi ne domin shirin zama Sarkin Zazzau na 19.

Ya kara da cewa:

“Ban ga dalilin da zai sa na tara dukiya ba, saboda mahaifina bai bar komai ba, ba ni da komai. Kuɗin da ke cikin asusuna kawai su ne alawus ɗin ma’aikatan diflomasiyya da ake ba mu kamar albashi duk wata; shi ke nan."

Sarkin ya ce a halin yanzu yana da gida guda a Zaria da wani a Abuja, yana mai cewa bai taba sha’awar tara abubuwan duniya ba.

Bamalli ya ce falsafarsa ta shugabanci ba ta dace da neman dukiya da tara kayan duniya ba, domin shugabanci a wajensa hidima ne.

Ya ce ya rantse da Alƙur’ani cewa zai kasance mai adalci da gaskiya ga mutanen masarautar Zazzau.

Kara karanta wannan

'Ni na ci zaɓe a 2023': Kalaman Obi da suka dugunzuma fadar shugaban ƙasa

Sarkin Zazzau ya yaba wa Uba Sani

Mun ba ku labarin cewa Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Bamalli, ya goyi bayan karin albashin sarakunan gargajiya da aka shirya a Kaduna.

Bamalli ya ce karin zai taimaka wa masarautun gargajiya, yayin da ya bayyana cewa Zazzau ta warware fiye da shari’o’in farar hula 2,000.

Sarkin ya ce masarautar Zazzau na hada kai da gwamnati da jami’an tsaro, tare da bayar da rahotannin sirri domin zaman lafiya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jarida ne da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.