Shin da Gaske Gwamnatin Edo Ta Hana Davido Shiga Jihar bayan Kin ba Gwamna Hakuri

Shin da Gaske Gwamnatin Edo Ta Hana Davido Shiga Jihar bayan Kin ba Gwamna Hakuri

  • Gwamnatin Jihar Edo ta yi magana kan rahoton cewa ta hana fitaccen mawakin Afrobeat, David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, shiga jihar
  • Kwamishinan Yaɗa Labarai da Dabarun Sadarwa, Kassim Afegbua, ya ce Edo gida ce ga kowa ba tare da la’akari da ra’ayinsa ko siyasarsa ba
  • Gwamnatin ta ce za ta yi maraba da Davido kuma a shirye take ta haɗa gwiwa da shi idan ya shirya yin wasa a jihar nan gaba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Edo - Gwamnatin Jihar Edo ta musanta cewa ta hana fitaccen mawakin Afrobeat, David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, shiga jihar.

Kwamishinan Yaɗa Labarai da Dabarun Sadarwa na jihar, Kassim Afegbua, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, 21 ga watan Agustan 2026.

Kara karanta wannan

Minista ya fasa kwai, an ji yadda ake shirin ƙarawa Atiku 'hawan jini' kafin zaben 2027

Gwamnati ta ce ba ta hana Davido shiga Edo ba
Gwamna Monday Okpebholo da mawaki Davido Hoto: @m_akpakomiza, @davido
Source: Twitter

Gwamnatin Edo ta musanta haramcin

A cikin sanarwar, Afegbua ya ce gwamnatin jihar ba ta da hannu a irin wannan mataki, yana mai bayyana wanda ya sanar da haramcin a matsayin maƙiyin Jihar Edo da kuma mai yaudara, cewar rahoton The Punch.

"Maƙiyanmu sun sake farfaɗowa; ba mu hana Davido shiga Jihar Edo ba. Wanda ya sanar da wannan haramcin maƙiyin Jihar Edo ne, ɗan kwaikwayo kuma ɗan damfara."
“Gwamnatin Jihar Edo ta nesanta kanta daga irin wannan ɗabi’a ta ƙiyayya, kuma tana son ƙara bayyana cewa Jihar Edo gida ce ga kowa, ba tare da la’akari da imaninsa, ra’ayinsa na siyasa, kusancinsa da wata ƙungiya ko kuma alaƙarsa ta doka ba."
“A zahiri, idan Davido ya yi niyyar yin wasa a Jihar Edo nan gaba, jihar za ta kasance a shirye ta yi haɗin gwiwa da shi.”

Edo ta ce Davido ɗanta ne

Kwamishinan ya ce Gwamna Monday Okpebholo mutum ne da ke iya tafiyar da al’amura daidai da ra’ayoyi da rukunin jama’a daban-daban da ke jihar.

Kara karanta wannan

Bayan takun saka, hadimin gwamna ya hana Davido shiga jiharsa sai bayan mulki

“Davido ɗaya ne daga cikin fitattun ’ya’yanmu, domin mahaifiyarsa ’yar asalin Jihar Edo ce. Shi abin koyi ne, kuma muna farin cikin kasancewa tare da shi."
“Idan yana son ziyartar Jihar Edo, za mu yi farin cikin tarbarsa da kuma shirya masa liyafa. Abin da ya faru a Jihar Osun sakamakon zaɓen makon da ya gabata siyasa ce kawai, ba wani abu na kashin kai ba. Babu wani abu na kashin kai a cikin maganganun da suka ƙara ƙaimin yakin neman zaɓen."
“Davido matashi ne da ya kasance ɗaya daga cikin jakadun Najeriya a duniya, yana ƙara wa ƙasar daraja tare da gina hanyoyin fahimtar juna tsakanin ɓangarorin siyasa da zamantakewa daban-daban.” In ji shi.
Gwamnatin Edo ta yi magana kan Davido
Mawakin Afrobeats, David Adeleke da aka fi sani da Davido Hoto: Davido
Source: Facebook

Afegbua ya ce gwamnatin jihar na farin ciki da yadda Davido ke gudanar da harkokinsa, da jajircewarsa da kuma yadda yake samun nasara a masana’antar waƙa.

"A matsayinta na gwamnati, muna farin ciki da ɗabi’arsa, jajircewarsa da kuma yadda yake samun nasara cikin tsari a masana’antar waƙa. A zahiri, muna masa fatan samun lambar yabo ta Grammy.” In ji shi.

Kara karanta wannan

Mahaifi ya kona 'yar cikinsa saboda malalar fitsarin kwance kullum a gadonsu

Davido ya ki ba Gwamna Okpebholo hakuri

A wani labarin kuma, kun ji cewa David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, ya ce ba zai ba Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo, hakuri ba.

Davido ya ce bai aikata wani abu mara kyau ba wajen wallafa sakamakon jarabawar WAEC na gwamnan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng