ICPC ta Miƙa Wa Tinubu Rahoton Abubuwan da Ta Gano kan Badakalar Kafa Hukumar Bogi

ICPC ta Miƙa Wa Tinubu Rahoton Abubuwan da Ta Gano kan Badakalar Kafa Hukumar Bogi

  • Hukumar ICPC ta mika wa Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu rahoton wucin gadi kan binciken PFIPC ta ake ta magana a kanta
  • Hukumar ta ce Prince Adeyemi Matthew bai taba samun nadi daga gwamnatin tarayya a hukumance ba
  • Ta bayyana cewa PFIPC ba ta da tushe a doka ko umarnin zartarwa, yayin da takardun nadin da aka yi anfani da su duk na jabun ne

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Hukumar Yaki da Rashawa (ICPC) ta kammala bincike kan hukimar Presidential Foreign Intervention Promotion Council (PFIPC) da aka ce ta bogi ce.

Bayan kammala bincike, hukumar ICPC ta tabbatar da cewa ta mika rahoton wucin gadi ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Bola Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnatin tarayya Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Shugaban ICPC, Musa Adamu Aliyu, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa bayan mika rahoton, kamar yadda Daily Trust ta rahoto.

Kara karanta wannan

Dalilan EFCC na garkame asusun gwamnatin Osun kafin zabe

Ya ce binciken ya tabbatar da cewa Prince Adeniyi Adeyemi Matthew, wanda ke ikirarin shi ne shugaban hukumar bogi, bai taba samun nadi daga fadar shugaban kasa ko wata hukuma ta gwamnatin tarayya ba.

PFIPC ba ta da tushe a doka

Bayan ce-ce-ku-cen da suka dabaibaye wannan hukuma, Shugaba Tinubu ya umarci ICPC a ranar 7 ga Yuli da ta gudanar da bincike tare da gabatar da rahotonta cikin kwanaki 30.

Shugaban ICPC ya ce binciken ya gano cewa:

"An tabbatar cewa Adeyemi Matthew bai taba samun nadi daga gwamnatin tarayya ko wata hukuma ta gwamnati ba."

A cewarsa, takardar nadin da Adeyemi ya gabatar ta jabu ce, haka ma sauran takardun da aka yi anfani da su wajen gudanar da ayyukan wannan haramtacciyar hukuma.

Ya kwace tsohon ofishin gwamnati

Shugaban ICPC ya bayyana cewa Adeyemi ya yi anfani da tsohon ofishinnPresidential Economic Advisory Council wajen kirkirar wannan hukuma ta bogi, sannan ya kwace ofishinta ba bisa ka'ida ba.

Kara karanta wannan

Malamin addini ya tubure kan dokar gwamnatin Tinubu na hana wa'azi, ya sha alwashi

A rahoton Vanguard, ya ce:

"Mun gano cewa an balle makullin ofishin, sannan ya shiga ciki ya mamaye wurin. Daga nan ne ya fara gudanar da ayyukan wannan hukuma ta bogi da kuma yaudarar jama'a."

Ya kuma ce binciken ya nuna akwai gibin tsarin tantancewa da sa ido tsakanin hukumomin gwamnati, lamarin da Adeyemi ya yi anfani da shi saboda sakacin wasu jami'an gwamnati.

ICPC.
Hedkwatar hukumar yaki da rashawa ta ICPC da ke Abuja Hoto: ICPC
Source: Facebook

ICPC ta ba da shawarwari

Hukumar ICPC ta ba da shawarar gurfanar da Adeyemi Matthew a gaban kotu bisa laifukan da ake zarginsa da su.

Ta kuma bukaci a hukunta jami'an gwamnati da bincike ya nuna sakacinsu ya taimaka wajen bai wa wannan hukuma ta bogi damar gudanar da ayyukanta.

ICPC ta kuma ba da shawarar a sake fasalin tsarin kula da hukumomin gwamnati domin karfafa hanyoyin sa ido da hana irin wannan lamari sake faruwa a nan gaba.

PFIPC: Yadda aka damfari dan kasuwa N400m

A wani labarin, kun ji cewa wani dan kasuwa, Gbenga Collins ya ce ya ba Adeniyi Adeyemi N400m domin a saukaka ba kamfaninsa kwangilar gyara da samar da kayan daki.

Collins ya ce ya dauki PFIPC a matsayin halastacciyar hukumar gwamnatin tarayya saboda Adeyemi na aiki daga wani ofishi da ke sakatariyar tarayya a Abuja .

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262