PFIPC: Kamfanin Amurka Ya Kawo Dauki ga Shugaban Hukumar Bogi da Ake Ta Surutu a Najeriya

PFIPC: Kamfanin Amurka Ya Kawo Dauki ga Shugaban Hukumar Bogi da Ake Ta Surutu a Najeriya

  • Kamfanin Von Batten-Montague-York ya bayyana cewa a shirye yake ya taimaka wa Adeniyi Adeyemi wajen neman mafaka a Amurka
  • Ya ce an riga an sanar da wasu manyan jami'an gwamnatin Shugaba Donald Trump kan lamarin kafa hukumar bogi
  • Kamfanin ya ce duk da babu wata doka da ta kafa PFIPC, amma yadda ta gudanar da ayyukanta ya nuna akwai alamar tambaya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Kamfanin Von Batten-Montague-York, LC da ke Amurka ya tsoma baki kan badakar kafa hukumar Presidential Foreign Intervention Promotion Council (PFIPC) ba tare da izinin gwamnatin Najeriya ba.

Kamfanin, wanda dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar ADC, Atiku Abubakar ya dauko haya, ya ce a shirye yake ya taimakawa Adeniyi Adeyemi wanda ake zargin ya jagoranci kafa hukumar bogi.

Kara karanta wannan

"Ba boyewa na yi ba"; Adeyemi ya bayyana abin da yake tsoro kan badakalar PFIPC

Adeyemi.
Shugaban hukumar bogi da ke ta surutu a kanta, Adeniyi Adeyemi Hoto: Adeniyi Adeyemi
Source: Facebook

Wanda ya kafa kamfanin, Karl Von Batten, ne ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X yayin da yake martani kan rikicin da ya dabaibaye PFIPC.

Ya bayyana cewa a shirye yake ya taimaka wa Adeniyi Adeyemi, wanda ke fuskantar bincike daga hukumomin Najeriya, wajen neman mafakar siyasa da kariyar Amurka

Amurka za ta iya shiga lamarin PFIPC

Von Batten ya ce hukumomin Amurka za su iya shiga binciken lamarin saboda wani ɓangare na kasafin kuɗin Najeriya na samun tallafi daga rancen Bankin Duniya, wanda Amurka ita ce babbar mai ruwa da tsaki a cikinsa.

Ya ce duk da cewa PFIPC ba ta da wata doka da ta kafa ta ko kuma sanarwar shugaban ƙasa, ta gudanar da ayyukanta kamar hukumar gwamnati, inda aka ware mata kuɗi a kasafin 2026, ta samu ofis a sakatariyar tarayya tare da ɗaukar ma'aikata.

Kamfanin Amurka ya goyi bayan Adeyemi

Kara karanta wannan

PFIPC: Yadda 'yan sanda suka bankado ma'aikatar bogi a karkashin gwamnatin Tinubu

A wani saƙo da ya wallafa ranar Litinin, Von Batten ya ce ya tattauna da Adeyemi kuma ya gano cewa mutum ne mai gaskiya kuma abin yarda.

Ya ce zarge-zargen da Adeyemi ya yi sun isa su sa hukumomin Amurka su fara bincike kan wannana badaƙala.

Von Batten ya ce:

"Bayan tattaunawarmu, na yi imanin cewa zarge-zargen da ya gabatar sun cancanci Majalisar Dokokin Amurka, Ma'aikatar Harkokin Waje, Ma'aikatar Kuɗi da sauran hukumomin Amurka su bincika.

An gargadi gwamnatin Najeriya

Ya ƙara da cewa ya riga ya sanar da wasu manyan jami'an tawagar Shugaban Amurka Donald Trump game da lamarin, tare da bayyana cewa za su fara yi wa mambobin Majalisar Dokokin Amurka bayani a cikin wannan makon.

Kamfanin ya ce idan wani abu ya samu Adeyemi ko iyalansa yayin da yake shirin tattaunawa da hukumomin Amurka, za a ɗora alhakin hakan kan Shugaba Bola Tinubu kuma a nemi hukunta shi a Amurka.

Shugaba Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnatin Najeriya Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Adeyemi ya aika sako ga Tinubu

An ji cewa shugaban hukumar bogi ta PFIPC, Adeniyi Adeyemi ya nuna rashin amincewa da bai wa hukumar ICPC umarnin bincikar badakalar ma'aikatarsa.

Kara karanta wannan

Adeyemi: Shugaban ma'aikatar bogi ya aika wasika ga Tinubu ana batun kai shi kotu

Ya bukaci a kafa kwamitin bincike mai zaman kansa domin gano gaskiya, yana zargin cewa gwamnatin tarayya ta riga ta wanke Femi Gbajabiamila.

A cewarsa, hanyar da ta fi dacewa wajen gano gaskiyar lamarin ita ce kafa kwamitin bincike mai zaman kansa, wanda ba shi da alaka da wata hukumar gwamnati.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262